Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
Published: 3rd, June 2025 GMT
Daya daga cikin manyan-manyan jami’an gwamnatin tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana cewa: “Babu tantama gwamnatin HK Isra’ila ta tafka laifukan yaki a kan Falasdinawa a zirin Gaza da ta killace.
Matthew Miller wanda ya yi aiki a matsayin kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka tun daga 2023 har zuwa karshen gwamnatin Joe Biden, ya fada wa tashar talabijin ta Sky News kan cewa; Isra’ilan ta tafka laifukan yaki.
Da aka yi masa tambaya a kan yakin Gaza a fadar White House, Miller ya ce; An yi ta samun tsabani dangane da yakin, sabani manya-manya wani lokacin kuma kananan sabani, kan yadda za a kare dangantakar Amurka da HK Isra’ila duk tare da abinda take aikatawa.”. Amma Miller ya tabbatar da cewa HK Isra’ilan ta tafka laifukan yaki wanda babu shakka a cikin hakan..
Da aka tambaye shi a kan, ko me ya sa a lokacin suke Mulki bai bayyana cewa HK Isra’ila tana aikata laufkan yaki ba? Sai ya amsa da cewa:
“Idan mutum yana cikin gwamnati, ba ya bayyana ra’ayinsa na kashin kansa, yana bayyana ra’ayin gwamnatin Amurka ne.”
Haka nan kuma ya ce; Aikin mai magana da yawun gwamnati, ko dai ka zama mai Magana da yawun shugaban kasa, ko gwmanatin kasar, amma idan baka cikin gwamnati, to za ka iya fadar ra’ayinka.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: HK Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10
Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwanaki goma domin bikin Babbar Sallah da za a yi ranar Juma’ar wannan makon.
Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, a cikin wata sanarwa ta bayyana cewa makarantun za su fara hutun ne daga ranar Laraba, 4 ga watan nan na Yuni da muke ciki, zuwa ranar Lahadi, 15 ga wata.
Sanarwar ta kuma bukaci iyaye da ’ya’yansu suke makarantun kwana da su je da wuri domin daukar yaran a ranar Laraba.
Kwamishinan mai kula da ma’aikatar, Ali Makoda, ya kuma bukaci iyaye da su tabbata daliban sun dawo makaranta a kan kari bayan kare hutun Babbar Sallar.
An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a ZamfaraA sakonta na taya daliban murna da fatan za a yi Babbar Sallah lafiya, ma’aikatar ilimin ta bayyana cewa hutun ya yi daidai da jadawalin zangon karatu da ake ciki, kuma ba a canza shi ba.