HausaTv:
2025-07-03@03:59:10 GMT

Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa

Published: 18th, May 2025 GMT

Kasar Faransa ta mika iko na sansanin soja na Contre-Amiral Protet ga kasar Senegel, wanda shi ne sansanin soja na 3 da aka mikawa kasar a bana.

An mika sauran sansanoni biyu da suka hada da Marechal da Sanit-Exupery ne a watan Maris din da ya gabata, Kuma dukkan sansanonin na da mazauni ne a Dakar, babban birnin Senegal.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Faransa ya fitar, ta ce an tsara mika dukkan wasu sansanonin dake karkarshin ikon Faransa a Senegal a bana, biyo bayan yarjejeniyar da kasashen biyu suka yi.

A ranar 31 ga watan Disamban 2024, shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya sanar a jawabinsa na sabuwar shekara cewa, za a bukaci dakarun Faransa su fara janyewa daga kasar a bana.

A shekarun baya bayan nan dai kasashen Afrika sun yi ta kira da janye dakarun Faransa daga kasashensu.

Shi ma a jawabinsa na sabuwar shekara, shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara, ya gabatar da shirin ficewar dakarun Faransa daga kasarsa.

Tun tuni daga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka raba gari da kasar ta Faransa tare da yanke alakar soji a tsakaninsu, sai kuma kasar Chadi wacce ta bi sahu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Jakadan Pakistan a kasar Sin, Khalil Rahman Hashimi ya ce, “sabuwar dokar ta bayar da karin kariya har ma da wani sauki na musamman ga kamfanoni masu zaman kansu a kasar Sin. Akwai tanade-tanade da dama a kasar Sin wadanda suke bayar da kwarin gwiwa ga kamfanoni masu zaman kansu don su iya bunkasa harkokinsu da kuma ba da gagarumar gudummawa ga tattalin arzikin kasar Sin. Akwai samun moriya da dama da kuma goyon bayan gwamnati har ma da ba da kariya ta fuskar shari’a ga kamfanoni masu zaman kansu.”

Shi ma jakadan Nepal a kasar Sin, Krishma Prasad Oli ya ce, “dokar ta sahale wa kamfanoni su gudanar da ayyukansu ba tare da wani matsi ba. Akwai babbar dama da aka samu a halin yanzu saboda akwai takamaimiyar doka da ta bayar da damar shigar kamfanonin kasashen ketare cikin hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin kuma suna iya yin aiki tare.”

Tuni dai aka fara ganin alherin sabuwar dokar bisa yadda ’yan kasashen waje ke tururuwar kafa kamfanoni da harkokinsu na kasuwanci a kasar ta Sin. Sakamakon amanna da kafuwar dokar da kuma fara aikinta, an kafa kamfanoni da ’yan kasuwa na kasashen waje suka zuba jarinsu fiye da 24,000 a cikin watanni biyar na bana kamar yadda ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta tabbatar a ’yan kwanakin nan. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba