Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
Published: 6th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da kasashen makwabtanta
Shugaban kasar Iran Mas’oud Pezeshkian ya jaddada cewa: “Babban burinsu shi ne neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da makwabtansu, kuma ba su dauke da kiyayya a kansu.
Shugaba Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a gaban taron majalisar kwararru masu zaben Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran a jiya litinin, ya jaddada wajabcin kiyaye hadin kai da hadin kai a cikin kasar da dukkan al’ummar musulmi. Yana mai cewa: “Tare da haɗin kan kasa, za su iya magance dukkan matsalolin cikin gida.” Sannan ya kuma yi kira da a kaucewa duk wani mataki da zai kawo cikas ga wannan hadin kai tare da daukar hanyar kawo sauyi a maimakon fada da juna.
Shugaba Pezeshkian ya ci gaba da cewa: Al’ummun da ke rayuwa a wannan ƙasar, ko da wane irin ƙabila ne, ko jinsi, ko kuma imaninsu, suna da hakkin gudanar da mu’amala a kan tubalin gaskiya da ‘yancin yin adalci da kuma samun adalci daga gwamnati.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi kan kada a kuskura a shiga tsakanin yaƙin da Iran da Isra’ila ke fafatawa ta hanyar amfani da ƙarfin soji.
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi gargadi kan duk wani “shiga tsakani na soji”, a yankin Gabas ta Tsakiya, inda manyan abokan gaba Isra’ila da Iran ke musayar wuta a rana ta shida.
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar DangoteIta ma ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta bukaci bangarorin biyu, da su kare fararen hula yayin da adadin mace-mace da jikkata ke ci gaba da karuwa.
Babbar sakatariyar ƙungiyar ta kasa da kasa, Agnes Callamard wadda ta yi wannan kira, ta buƙaci Iran da Isra’ila da su martaba haƙƙoƙin jama’a, tare da tabbatar da cewa ba fararen hula a ƙasashen biyu ne ake gasa wa tsakuwa a hannu sakamakon wannan rikici ba.
Rikicin dai ya fara ne a ranar Juma’a, lokacin da Isra’ila ta ƙaddamar da wani gagarumin harin bama-bamai wanda ya sanya Iran mayar da martani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa.
Tuni dai jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta amince da ƙarfa-ƙarfan zaman lafiya ba, yana mai gargaɗin Amurka cewa muddin ta kai musu hari, to za ta ɗanɗana kuɗarta.
Kalamansa na zuwa ne a yayin da Isra’ila ta ce ta kai hari kan wurare 40 a cikin Iran a wannan Larabar da suka haɗa da masana’antar ƙera makamai, yayin da ita ma Iran ta kadddamar da farmakin jirage marasa matuka kan Isra’ila.
A ɓangare guda, Rasha da Amurka na ganawa da juna da zummar lalubo zaren warware rikicin kamar yadda mataimakin Ministan Harkokin Wajen Rasha, Sergei Ryabkov ya bayyana.
Tun da farko ya gargaɗin cewa, muddin Amurka ta shiga cikin yaƙin kai-tsaye domin taimaka wa Isra’ila, to babu shakka hakan zai sake jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin ruɗani.