Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
Published: 6th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da kasashen makwabtanta
Shugaban kasar Iran Mas’oud Pezeshkian ya jaddada cewa: “Babban burinsu shi ne neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da makwabtansu, kuma ba su dauke da kiyayya a kansu.
Shugaba Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a gaban taron majalisar kwararru masu zaben Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran a jiya litinin, ya jaddada wajabcin kiyaye hadin kai da hadin kai a cikin kasar da dukkan al’ummar musulmi. Yana mai cewa: “Tare da haɗin kan kasa, za su iya magance dukkan matsalolin cikin gida.” Sannan ya kuma yi kira da a kaucewa duk wani mataki da zai kawo cikas ga wannan hadin kai tare da daukar hanyar kawo sauyi a maimakon fada da juna.
Shugaba Pezeshkian ya ci gaba da cewa: Al’ummun da ke rayuwa a wannan ƙasar, ko da wane irin ƙabila ne, ko jinsi, ko kuma imaninsu, suna da hakkin gudanar da mu’amala a kan tubalin gaskiya da ‘yancin yin adalci da kuma samun adalci daga gwamnati.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ISWAP Sun Kai Hari Sansanin Sojoji A Yobe
Wakilinmu ya ce mayaƙan “Operation HADIN KAI” sun fafata da maharan lokacin da suka kai hari Buni Gari.
Rundunar sojin ƙasa ta tabbatar da faruwar lamarin a shafinta na sada zumunta da safiyar yau Asabar.
A cewarta, “Mayaƙan Operation HADIN KAI suna ci gaba da fafatawa da mayaƙan ISWAP a Buni Yadi.”
Rahotannin sirri sun bayyana cewa jami’an sojin sun samu taimako daga mafarauta da ƴan bijilanti kafin daga baya maharan su gudu.
Har yanzu, ba a san adadin asarar da aka yi ba sakamakon harin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp