Da safiyar jiya Lahadi bisa agogon wurin, aka kammala horon hadin gwiwa tsakanin sojojin saman kasashen Sin da Masar mai suna “Shaho na wayewar kai-2025” cikin nasara, a wani sansanin sojojin saman Masar, wanda ya kwashe kwanaki guda 18.

 

Wannan horon na hadin gwiwa shi ne karo na farko da rundunar sojin saman kasar Sin ta aike da dakaru zuwa kasashen Afirka domin ba da horon hadin gwiwa.

A yayin horon na hadin gwiwa, sojojin saman kasashen Sin da Masar sun tattauna tare da yin musayar ra’ayi kan nau’o’in horarwa, da dabarun yaki da jiragen sama, da samar da man fetur a sama da dai sauransu, kuma sun samu nasarar kammala horarwa kan ayyukan sarrafa jiragen sama, da kiyaye tsaron sararin sama, da ceton mutane a fagen yaki, da yin darussan hadin gwiwa da dai sauransu, wannan wani mafari ne da kuma ci gaba a kan hanyar hadin gwiwar soji tsakanin kasashen biyu. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Tawagar kasar Sin a taron birnin Geneva, ta shaidawa kungiyar cinikayya ta duniya WTO, cewa kasar ta fadada matakinta na rage harajin fito da take karba daga kasashe masu karancin karfin tattalin arziki, daga kaso 98 bisa dari zuwa kaso 100 bisa dari.

A jiya Laraba ne tawagar ta Sin ta bayyana wannan albishir, inda ta ce baya ga janye dukkanin harajin fito baki daya, Sin ta sha alwashin kara aiwatar da matakai na ingiza cinikayyar hajoji, da karfafa kwarewar aiki, da aiwatar da kwasa-kwasai na horar da sana’o’in fasaha a kasashen Afirka masu raunin tattalin arziki.

Kazalika, tawagar ta Sin ta ce wadannan matakai na da nufin samar da sabbin damammakin habaka ci gaban wannan rukuni na kasashen Afirka, tare da bayar da gudummawar daidaitawa, da ingiza ci gaban cinikayya tsakanin sassan kasa da kasa.

Membobin kungiyar WTO sun jinjinawa wannan albishir na tawagar Sin, yayin da wakilai daga kasashen Afirka masu raunin tattalin arziki, da sauran sassan kasa da kasa suka bayyana godiya game da hakan, suna masu nuni da tarin kalubale, da yanayin rashin tabbas da kasashe masu tasowa ke fuskanta a duniya. Har ila yau, membobin WTOn sun yi kira ga karin kasashen duniya da su yi koyi da kasar Sin, wajen samar da manufofi masu dacewa, da tallafin horar da kwararru, da tallafawa rukunin kasashe masu karancin karfin tattalin arziki, ta yadda za a iya bunkasa cinikayya mai dorewa, da game dukkanin sassan kasa da kasa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki
  • Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi
  • Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta