Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani
Published: 5th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya caccaki tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Abdullahi Baffa Bichi da cewa maƙaryaci ne da ba shi da “kunya”.
Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taro da ya yi tare da ilahirin kansiloli 484 da ke fadin jihar a ranar Lahadi da maraice.
Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a SakkwatoAbba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.
Da ya ke jawabi a wajen taron da kansilolin, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci satar kudin al’umma ba.
A cewarsa, yana jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al’umma, inda ya jaddada cewa “ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu,”
Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da ayyuka domin jin dadin al’ummar Kano.
Abba ya mayar da martani kan zarge-zargen da Baffa Bichi ya yi cewa gwamnatin Jihar ta Kano tana tafka laifuka na cin hanci da rashawa fiye da gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, ta musanta dukkan zarge-zarge waɗanda ta bayyana a matsayin “abin dariya”.
“Zarge-zarge ƙarya ce tsagwaronta kuma abin dariya, Baffa Bichi babban maƴaryaci ne, kuma dukkan abin da ya faɗa ƙarya ce ziryan,” in ji Gwamnan.
“Musamman, Gwamna ya yi watsi da zargin cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, shugaban Tsarin Kwankwasiyya, yana karɓar naira biliyan biyu duk wata daga gwamnatin Jihar Kano.
Gwamna Abba Yusuf ya bayyana wannan zargi a matsayin “ƙololuwar ci-da-zuci na siyasa da rashin gaskiya.”
Gwamnan ya ce Baffa Bichi ya kwashe fiye da shekara ɗaya a cikin gwamnatinsa amma bai yi waɗannan zarge-zarge ba sai bayan an sallame shi daga aiki bisa rashin iya aiwatar da ayyukansa, yana mai cewa da a ce da gaske yake da sai ya yi zarge-zargen a lokacin da yake cikin gwamnati.
Ya ce zai ci gaba da gudanar da mulki cikin adalci, yana mai yin kira ga al’ummar Jihar Kano ta yi watsi da irin waɗannan zarge-zarge na ‘yan siyasar da ska rasa tasiri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso zarge zarge a gwamnatin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na yaki da gurbacewar kasa, zaizayar kasa da sauran kalubalen muhalli.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin kaddamar da wani katafaren shirin dashen itatuwa, inda za a dasa itatuwa miliyan 5 da rabi a fadin jihar, wanda aka gudanar a karamar hukumar Makoda.
Ya ce babban makasudin wannan shirin shi ne a magance dimbin kalubalen muhalli da ke addabar al’ummar jihar Kano.
Gwamna Yusuf ya jadadda cewa wadannan kalubalen na haifar da babbar matsala ga al’umma.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta bayar da duk wani tallafin da ya dace don shayar da ‘ya’yan itatuwan, ta yadda za su yi girma da kuma cim ma burin da aka yi niyya. Wannan tallafi yana da mahimmanci don nasarar shirin.
Ya bukaci dukkan shugabannin kananan hukumomi 44, shugabannin gargajiya, da jami’an ci gaban al’umma (CDOs) da su sanya hannu a cikin wannan shirin, inda ya ce shigar su na da matukar muhimmanci wajen cimma manufofin shirin.
“Idan aka kula da kyau itatuwan da aka dasa ta wannan shiri za su taka rawar gani wajen magance sauyin yanayi da batutuwan da ke da alaka da hakan. Hakan ya yi dai-dai da manyan manufofin jihar Kano.”
Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yaba da kudurin Gwamna Yusuf na tallafawa kokarin ma’aikatar wajen dakile matsalolin muhalli.
Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, wanda ya wakilci Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II ya jaddada goyon bayan Masarautar kan shirin dashen itatuwa.
Taron ya gabatar da bayar da kyautuka ga mutanen da suka bayar da gudunmawa sosai wajen tallafawa al’ummarsu.
Wannan amincewa yana aiki azaman abin ƙarfafawa ga wasu don shiga cikin ayyukan muhalli.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO