Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani
Published: 5th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya caccaki tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Abdullahi Baffa Bichi da cewa maƙaryaci ne da ba shi da “kunya”.
Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taro da ya yi tare da ilahirin kansiloli 484 da ke fadin jihar a ranar Lahadi da maraice.
Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a SakkwatoAbba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.
Da ya ke jawabi a wajen taron da kansilolin, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci satar kudin al’umma ba.
A cewarsa, yana jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al’umma, inda ya jaddada cewa “ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu,”
Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da ayyuka domin jin dadin al’ummar Kano.
Abba ya mayar da martani kan zarge-zargen da Baffa Bichi ya yi cewa gwamnatin Jihar ta Kano tana tafka laifuka na cin hanci da rashawa fiye da gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, ta musanta dukkan zarge-zarge waɗanda ta bayyana a matsayin “abin dariya”.
“Zarge-zarge ƙarya ce tsagwaronta kuma abin dariya, Baffa Bichi babban maƴaryaci ne, kuma dukkan abin da ya faɗa ƙarya ce ziryan,” in ji Gwamnan.
“Musamman, Gwamna ya yi watsi da zargin cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, shugaban Tsarin Kwankwasiyya, yana karɓar naira biliyan biyu duk wata daga gwamnatin Jihar Kano.
Gwamna Abba Yusuf ya bayyana wannan zargi a matsayin “ƙololuwar ci-da-zuci na siyasa da rashin gaskiya.”
Gwamnan ya ce Baffa Bichi ya kwashe fiye da shekara ɗaya a cikin gwamnatinsa amma bai yi waɗannan zarge-zarge ba sai bayan an sallame shi daga aiki bisa rashin iya aiwatar da ayyukansa, yana mai cewa da a ce da gaske yake da sai ya yi zarge-zargen a lokacin da yake cikin gwamnati.
Ya ce zai ci gaba da gudanar da mulki cikin adalci, yana mai yin kira ga al’ummar Jihar Kano ta yi watsi da irin waɗannan zarge-zarge na ‘yan siyasar da ska rasa tasiri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso zarge zarge a gwamnatin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria