Aminiya:
2025-06-20@17:11:15 GMT

Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani

Published: 5th, May 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya caccaki tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Abdullahi Baffa Bichi da cewa maƙaryaci ne da ba shi da “kunya”.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taro da ya yi tare da ilahirin kansiloli 484 da ke fadin jihar a ranar Lahadi da maraice.

Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato

Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

Da ya ke jawabi a wajen taron da kansilolin, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci satar kudin al’umma ba.

A cewarsa, yana jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al’umma, inda ya jaddada cewa “ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu,”

Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da ayyuka domin jin dadin al’ummar Kano.

Abba ya mayar da martani kan zarge-zargen da Baffa Bichi ya yi cewa gwamnatin Jihar ta Kano tana tafka laifuka na cin hanci da rashawa fiye da gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, ta musanta dukkan zarge-zarge waɗanda ta bayyana a matsayin “abin dariya”.

“Zarge-zarge ƙarya ce tsagwaronta kuma abin dariya, Baffa Bichi babban maƴaryaci ne, kuma dukkan abin da ya faɗa ƙarya ce ziryan,” in ji Gwamnan.

“Musamman, Gwamna ya yi watsi da zargin cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, shugaban Tsarin Kwankwasiyya, yana karɓar naira biliyan biyu duk wata daga gwamnatin Jihar Kano.

Gwamna Abba Yusuf ya bayyana wannan zargi a matsayin “ƙololuwar ci-da-zuci na siyasa da rashin gaskiya.”

Gwamnan ya ce Baffa Bichi ya kwashe fiye da shekara ɗaya a cikin gwamnatinsa amma bai yi waɗannan zarge-zarge ba sai bayan an sallame shi daga aiki bisa rashin iya aiwatar da ayyukansa, yana mai cewa da a ce da gaske yake da sai ya yi zarge-zargen a lokacin da yake cikin gwamnati.

Ya ce zai ci gaba da gudanar da mulki cikin adalci, yana mai yin kira ga al’ummar Jihar Kano ta yi watsi da irin waɗannan zarge-zarge na ‘yan siyasar da ska rasa tasiri.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso zarge zarge a gwamnatin

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

Sauran sun hada da: Danjuma Azi, Fwangje Bala Ndat, Salome Tanimu Wanglet, Namba Rimuyat, Nimchak Rims, Ishaku Maren da Paul Datugun.

 

Kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale, wanda ya tabbatar da kamun, ya ce bincike ya nuna cewa tsaffin ‘yan majalisar sun shafe watanni shida ne kawai a kan karagar mulki, sannan gwamnatin jihar ta siya musu motocin alfarma.

 

 

Bincike ya kuma nuna cewa, motocin da aka ce kudinsu ya kai Naira biliyan 2.5. Bayan sun sauka akan mukaminsu, sun tafi da motocin kuma duk kokarin da aka yi na su dawo da su, lamarin ya ci tura.

 

Sai da gwamnatin jihar ta sake sayo wa ‘yan majalisar na yanzu motocin da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan biyu.

 

Oyewale ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da tsohon shugaban majalisar da sauran mambobin a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • GORON JUMA’A 20-06-2025
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna