Aminiya:
2025-06-20@02:27:46 GMT

Boko Haram ta kashe sojoji 4 a Yobe

Published: 5th, May 2025 GMT

Rahotonni na cewa mayaƙan Boko Haram sun kai kashe dakaru huɗu yayin wani hari da suka kai sansanin soji a Jihar Yobe.

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun ƙaddamar da hari kan sansanin soji na “27 Task Force Brigade” da ke garin Buni Yadi, a yankin Ƙaramar Hukumar Gujba da tsakar daren Asabar.

Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato

Harin na zuwa ne kwana guda bayan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabashin ƙasar sun gudanar da taro a Damaturu, babban birnin jihar da nufin magance matsalolin yankin, ciki har da matsalar tsaro.

A baya-bayan nan mayaƙan Boko Haram da na ISWAP na neman dawo da hare-hare a yankin.

A cikin makon nan ma ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin wani hari da yayi sanadin mutuwar mutum 26 a Jihar Borno.

Ko makonni biyu da suka gabata sai da mayaƙan Boko Haram suka kai hari sansanin soji da ke yankin Chalie a Ƙaramar Hukumar Buni Yadi, inda suka kashe dakaru uku.

Sai dai a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ƙwato dazukan Arewa da ma sauran sassan ƙasar daga hannun masu garkuwa mtane domin karɓar kuɗin fansa da ‘yan ta’adda

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakaru Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Idan dai za a iya tunawa, a baya an kai hari gidan dangin Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 15 ga Afrilu, 2025, ba tare da an kama ko daya daga cikin maharan ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari