Ayatullah Khamenei: Babu Abinda ya fi hadin kai mahimmanci ga al’ummar musulmi
Published: 4th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa babu abin da ya fi mahimmanci kamar hadin kai ga al’ummar musulmi.
Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin masu shirya aikin hajji na iran.
A jawabin da ya gabatar, Ayatullah Khamenei ya yi tsokaci kan aikin Hajji da ake gudanarwa a kowace shekara, wanda ke hada al’ummar musulmi daga sassa daban-daban na duniya ba tare da la’akari da asali, launi, ko al’ada ba.
Jagoran ya ci gaba da cewa: Idan da al’ummar musulmi za su kasance da hadin kai, da matsalolin Falastinu da Gaza ba za su wanzu ba, kuma Yemen ba za ta kasance cikin irin wannan matsin lamba ba.
Ya kara da cewa, ya zama wajibi kasashen musulmi su hada kai, su kuma dakile wahalhalun da suke faruwa a zirin Gaza da Yemen.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: al ummar musulmi
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama
Kasar Spain ta bayyana abin da ke faruwa a Gaza a matsayin abin kunya ga bil’adama
Ministan harkokin wajen kasar Spain José Manuel Albares ya yi kira ga mahukuntan Isra’ila a ranar Alhamis da su bude mashigar ruwa na dindindin domin ba da damar kai agajin jin kai zuwa zirin Gaza, yana mai gargadin cewa; Bala’in jin kai a yankin da aka killace zai iya ta’azzara.
A nasa jawabin Albares ya jaddada cewa: Gaza na fuskantar yunwa sakamakon killacewar da haramtacciyar kasar Isra’ila ta mata, kuma abin da ke faruwa a wurin abin kunya ne ga bil’adama. Ya kara da cewa yunwa na ci gaba da lakume rayukan fararen hula a yankin a kowace rana.
Ministan na Spain ya jaddada cewa: “Fiye da yara 100,000 da jarirai 40,000 a Gaza na cikin hadarin yunwa,” yana mai kira da a tsagaita bude wuta cikin gaggawa don tabbatar da shigar da kayan abinci da magunguna ga al’ummar da aka killace su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci