Kafar United Daya Ta Kai Wasan Karshe A Gasar Europa League
Published: 4th, May 2025 GMT
Ƙafar Manchester United guda ta kai wasan ƙarashe na gasar Zakarun Turai ta Europa League bayan da ta doke Athletic Bilbao da ci 3-0 a Sifaniya.
Da fari wasan ya nuna kamar ba zai yi wa United kyau ba, to amma bayan minta 30 sai wasan ya sauya bayan da Harry Maguire ya yi wata bajinta tare da buga ƙwallo zuwa da’irar bilbao, lamarin da ya bai wa Casemiro damar zura ƙwallon farko a wasan.
Minti uku bayan nan ne United ta ƙara samun wata damar bayan da ɗan wasan bayan Bilbao, Dani Vivian ya yi wa Rasmus Hojlund ƙeta a yadi na 18, inda bayan duba na’urar taimaka wa alƙalin wasa ta VAR, aka bai wa Vivian jan kati tare da bai wa United bugun fenareti.
Bayan da Bruno ya buga fenaretin ya kuma ci, ya ƙara ta uku kafin tafiya hutun rabin lokaci bayan da ɗan wasan Bilbao ya yi kuskure.
A mako mai zuwa ne United – wadda kofin Europa ne kawai fatanta a wannan kaka – za ta karɓi baƙunci Bilbao a filin wasa na Old Trafford.
A ɗaya wasan na Europa kuwa, Tottenham ce ta samu nasara kan Bodø/Glimt da ci 3-1 a Ingila.
Masu nazarin ƙwallon ƙafa na hasashen buga wasan ƙarshe tsakanin ƙungiyoyin Ingila, United ta Tottenham a gasar ta Europa, wani abu da aka jima ba a gani ba.
Can ma a ƙaramar gasar ta Conference League, Chelsea ta samu nasarar doke Djurgården da ci 4-1, wadda ita ma ake hasashen za ta kai wasan ƙarshe na gasar.
A mako mai zuwa ne Arsenal za ta je gidan PSG a babbar gasar Zakatun Turai ta Champions League, da nufin ɗaukar fansa kan ci 1-0 da PSG ta yi mata a Emirates.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasanni
এছাড়াও পড়ুন:
Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya
A Alhamis din nan ne dai kasar ta Habasha ta fito da Shirin shuka bishiyoyi har miliyan 700 a rana daya, ta hanar shigar da miliyoyin mutanen kasar.
Fira ministan kasar ta Habasha Abi Ahmad yana son a rika tunawa da shi anan gaba ta hanyar shuka bishiyoyin da za su kai biliyan 50, daga nan zuwa shekara ta 2026.
Tun da safiyar jiya Alhamis ne dai miliyoyin mutanen kasar ta Habasha su ka fito zuwa wuraren yin shukar, inda su ka rika haka ramukan da za su yi dashen bishiyoyin.
Kakakin gwamnatin kasar ta Habasha, Tesfahun Gobezay ya bayyana cewa, da jijjifin Safiya, gabanin cikar karfe; 6;a.m, mutane miliyan 14.9 sun dasa bishiyoyin da sun kai miliyan 355.
Shi ma Fira MInistan kasar Abi wanda tun a 2019 ya yi fice da bunkasa dajukan kasar, ya walalfa sako a shafinsa na X yana cewa: Mun kaddamar da Shirin shuka bishiyoyi da safiyar yau,kuma manufarmu a wannan shekarar ita ce, shuka bishiyoyi miliyan 700.”
Mutane daban-dabnan ne su ka shiga cikin Shirin na shuka bishiyoyin, a sassa mabanbanta na kasar ta Habasha.
Wani kwararre a fagen dajuka a jami’ar Jimma ya nuna shakkunsa akan yiyuwar shuka bishiyoyi miliyan 700 a rana, yana mai cewa; Domin yin hakan da akwai bukatar mutane miliyan 34 su shiga, kuma kowane daya daga cikinsu ya shuka bishiya 20.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI July 31, 2025 Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci