Ƙungiyar mayaƙan ISWAP sun mamaye garin Buni Gari a daren Juma’a da ƙarfe 12:00 na dare, mahaifar Gwamna Buni da ke ƙaramar hukumar Gujba a Jihar Yobe inda suka kai wani harin ba zata a garin da kuma barikin soja ta 27 da ke garin.
Wata majiya mai tushe daga garin ta tabbatar da cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na daren Juma’a, inda maharan suka ƙona wani ɓangare na hedkwatar rundunar ta 27 da ke Buni Gari a Jihar ta Yobe.
Wannan gari na Buni Gari wadda bai wuce kilomita bakwai ba daga Buni Yadi hedkwatar ƙaramar hukumar ta Gujba wanda ke ɗauke da makarantar sojoji ta musamman kusan yanki ne da maharan ƙungiyoyin ‘yan Boko Haram da ISWAP suka fi kai kawo lokaci zuwa lokaci sakamakon kusancin da wani babban dajin da ya haɗa da dajin Sambisa.
Wasu mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa, lokacin da waɗannan ’yan ta’addan suka iso garin sun yi ta harba makamansu ta kowace kusurwa lura da cewar garin na gaɓar dazuzzukan da ke kewaye da shi kafin daga bisani su shiga wani ɓangare na barikin sojan inda suka ƙona wasu gine-gine na mazauna yankin.
Aminiya ta tattaro rahoton cewa, a halin yanzu jami’an soji da ke ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai sun yi artabu da waɗannan ’yan ta’adda da ake kyautata zaton ’yan ISWAP ne.
Wata majiya mai tushe daga rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar wani takaitaccen bayani da ta fitar a sahfinta na sada zumunta na X ( Twitter) a ranar Asabar.
Sai dai majiyar leƙen asiri na cewar, ’yan ta’addan sun kai hari a garin, inda suka riƙa harbe-harbe, amma cikin gaggawa sojojin tare da haɗin gwiwar mafarauta da ‘yan banga suka shiga tsakani inda suka shawo kan lamarin tare da fatattakar waɗannan ‘yan ta’addan.
Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani dangane da harin da kuma ko an yi asarar rayuka a hukumance.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC
Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta ce ta gano wata sabuwar dabarar satar kudi da wasu ’yan siyasa ke amfani da ita a yanzu ta hanyar amfani da ’yan damfara wadanda aka fi sani da ’yan yahoo a fadin kasar.
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede na wannan furuci ne yayin ganawa da manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Litinin.
Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — AtikuOlukoyede wanda ya ce wadannan matasa ’yan yahoo da suke zubar da kimar Nijeriya a idon duniya sun kuma faɗa dumu-dumu ta’adar nan ta garkuwar da mutane domin neman kuɗin fansa.
Ya bayyana cewa kaurin suna da ’yan yahoo suka yi a matsayin miyagu sun shafa wa kowane ɗan Nijeriya bakin fenti da duk inda suka shiga ake ɗari-ɗari da su a matsayin masu laifi.
Shugaban na EFCC ya ce a yanzu da zarar miyagun ’yan siyasa sun samu damar yin ruf da ciki a kan dukiyar kasa, sukan haɗa kai da waɗannan matasa ’yan yahoo-yahoo su boye kuɗaɗen a cikin wani asusun yanar gizo da ake kira wallet.
“Sau tari irin waɗannan ’yan siyasa sukan jibge ’yan yahoo a otel-otel su rika buɗe musu asusun ajiya na kirifto su boye biliyoyin kuɗaɗen da suka sata.”
Olukoyede ya buga misali da wani matashi mai shekaru 22 da hukumar ta kama yana yi wa ’yan siyasa irin wannan aika-aikar wanda aka gano ya samu tukwicin Naira biliyan biyar a tsawon watanni 18 kacal.