Aminiya:
2025-08-03@00:46:25 GMT

ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe 

Published: 3rd, May 2025 GMT

Ƙungiyar mayaƙan ISWAP sun mamaye garin Buni Gari a daren Juma’a da ƙarfe 12:00 na dare, mahaifar Gwamna Buni da ke ƙaramar hukumar Gujba a Jihar Yobe inda suka kai wani harin ba zata a garin da kuma barikin soja ta 27 da ke garin.

Wata majiya mai tushe daga garin ta tabbatar da cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na daren Juma’a, inda maharan suka ƙona wani ɓangare na hedkwatar rundunar ta 27 da ke Buni Gari a Jihar ta Yobe.

An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato

Wannan gari na Buni Gari wadda bai wuce kilomita bakwai ba daga Buni Yadi hedkwatar ƙaramar hukumar ta Gujba wanda ke ɗauke da makarantar sojoji ta musamman kusan yanki ne da maharan ƙungiyoyin ‘yan Boko Haram da ISWAP suka fi kai kawo lokaci zuwa lokaci sakamakon kusancin da wani babban dajin da ya haɗa da dajin Sambisa.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa, lokacin da waɗannan ’yan ta’addan suka iso garin sun yi ta harba makamansu ta kowace kusurwa lura da cewar garin na gaɓar dazuzzukan da ke kewaye da shi kafin daga bisani su shiga wani ɓangare na barikin sojan inda suka ƙona wasu  gine-gine na mazauna yankin.

Aminiya ta tattaro rahoton cewa, a halin yanzu jami’an soji da ke ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai sun yi artabu da waɗannan ’yan ta’adda da ake kyautata zaton ’yan ISWAP ne.

Wata majiya mai tushe daga rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar wani takaitaccen bayani da ta fitar a sahfinta na sada zumunta na  X  ( Twitter) a ranar Asabar.

Sai dai majiyar leƙen asiri na cewar, ’yan ta’addan sun kai hari a garin, inda suka riƙa harbe-harbe, amma cikin gaggawa sojojin tare da haɗin gwiwar mafarauta da ‘yan banga suka shiga tsakani inda suka shawo kan lamarin tare da fatattakar waɗannan ‘yan ta’addan.

Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani dangane da harin da kuma ko an yi asarar rayuka a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buni Gari ISWAP

এছাড়াও পড়ুন:

Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine

Wani sojan Amurka ya ba da shaida game da kisan wani yaro da sojojin mamayar Isra’ila suka yi a cibiyar bada agaji ta Rafah

Wani sojan Amurka da ke aiki a cibiyar rarraba kayan abinci a zirin Gaza ya yi furuci da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kai hari kan wani yaro Bafalasdine da ya yi tafiya mai nisan kilomita 12 a karkashin zafin rana, don neman kayan abincin agaji a yankin.

A cikin wata sheda mai ratsa jiki da ya bayar a cikin wani dan gajeren faifan bidiyo a Amurka, Private Anthony Aguilar ya ba da labarin wani lokaci da ba za a manta da shi ba cewa: Wani yaro siriri mai suna Amir, babu takalmi a kafarsa, ya yi tafiya mai nisa don isa wurin rarraba kayan agaji inda aka ba shi shinkafa da adasi inda ke ja a kasa.

Sojan Amurkan nan ya kara da cewa: Yaron nan ya matso kusa da shi, ya sumbaci hannunsa, ya ce, “Na gode.”

Bayan ‘yan mintoci, yayin da Amir ke tafiya tare da wasu fararen hula, sai sojojin mamayar Isra’ila sun harba barkonon tsohuwa da harsasai kan taron jama’ar, inda suka raunata Falasdinawa masu yawa tare da kashe Amir nan take.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja
  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Watsi Da Duk Wani Zarge-Zargen Neman Bata Mata Suna
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine