Pakistan Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Mai Cin Tazarar Kilo Mita Fiye Da 400
Published: 3rd, May 2025 GMT
Sojojin kasar Pakistan sun sanar da yin nasarar gwajin makamai mai linzami da ake harbawa daga kasa, wanda yake cin Zangon kilo mita 450.
Sanarwar sojojin kasar ta Pakistan ya kunshi cewa; Sun yi gwajin ne dai domin tabbatar da zama cikin shiri na sojoji, da kuma tabbatar da ingancin aikin makamin.
Gwajin makamin na sojojin Pakistan ya zo ne a daidai lokacin da ake zaman dar-dar a tsakaninta da kasar Indiya, bayan wani harin ta’addanci da aka kai a yankin Kashmir.
A ranar 22 ga watan Afrilu ne dai aka kai wani hari akan masu yawon bude ido a yankin na Kashmir wanda ya yi sanadiyyar kashe mutane 26. Da akwai fargabar cewar kasashen biyu za su tsunduma cikin wani sabon yaki,bayan da Indiya ta zargi Pakistan da cewa tana da hannun a wancan harin.
Pakistan dai ta kore cewa tana da hannu, tare da yin kira ga Indiya da ta kaucewa tsokana, domin za ta mayar da martanin da ya dace gwargwadon harin da za ta kai mata.
Mahukuntan kasar Pakistan sun gargadi Indiya akan cewa, su kwana da sanin cewa; Islamabad tana da makaman Nukiliya.
A yau Asabar an yi musayar wuta a tsakanin sojojin kasashen biyu a tsawon yankin da ya raba su a yankin Kashmir.
A jiya Juma’a mahukunta a yakin Kashmir sun yi kira ga mazauna yankin da su tanadi abincin da zai ishe su na tsawon watanni biyu,saboda tsoron yiyuwar barkewar yaki a tsakanin kasashen biyu masu karfin Nukiliya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin ta shirya tsaf wajen aiwatar da soke haraji da kashi 100 bisa 100 a kan kayayyakin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar jakadanci da kasar ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a fannin raya tattalin arziki.
A yau, wani jami’in ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ya gabatar da wani batu da ya dace da hakan. Inda ya bayyana cewa, a mataki na gaba, ma’aikatar kasuwanci za ta yi aiki tare da sassan da abin ya shafa, wajen inganta kulla yarjejeniyar hadin gwiwa ta fuskar tattalin arziki don samun ci gaba na bai-daya tare da kasashen Afirka bisa ka’idojin tuntubar juna da samun moriyar juna dai-dai-wa-daida. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp