“Siyasar da na sani ba ita ce abin da ke faruwa a yau ba. Siyasar da na sani ita ce gwagwarmayar muradun jama’a don tabbatar da cewa suna da kyakkyawar rayuwa a duk fannoni kamar ilimi, ruwa, kiwon lafiya, da sauransu. “Na kasance a siyasa tsawon shekaru 48 da suka gabata,” in ji shi.

Ya bayyana yanayin siyasa a matsayin wanda ke cike da rudani da son kai, yana mai jaddada cewa ‘yan siyasa da talakawa sun rikice.

“Saboda wannan, akwai rudani ga masu nema da kuma wadanda ake nema. Masu neman suna makancewa, ba su da imani ko tausayi. Manufarsu kawai ita ce tabbatar da matsayi a gare su. A halin yanzu, talakawa sun tsunduma ciki yunwa, talauci, da jahilci, don haka komai yana cikin rudani,” in ji Bafarawa.

Tsohon gwamnan ya kuma nuna matukar damuwa game da karuwar jahilci a tsakanin matasa, musamman a arewacin Nijeriya, yana mai gargadin cewa makomar yankin na cikin hadari.

“Duk lokacin da kuka cusa mutane cikin jahilci ta hanyar hana su ilimi, kun gama da su. A nan arewa, a gaskiya, kusan kashi 70 cikin 100 na matasanmu ba su da ilimi. Ta yaya wata kasa ko yanki za ta ci gaba ba tare da ilimi ba?” ya tambaya.

Bafarawa ya kare talakawa masu jefa kuri’a da ke karbar kudi a lokacin zabe, yana mai cewa mawuyacin halin tattalin arziki da suke fuskanta ya sa ba su da wani zabi.

A cewarsa, taimakon Allah ne kadai zai iya ceto Nijeriya daga kalubalen da take fuskanta a yanzu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu

Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.

Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Shugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.

“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.

“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”

Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai yi shekara takwas yana mulki – Afenifere
  • Kasar Sin Na Tantance Sakonnin Amurka Na Neman Tattaunawa A Kan Karin Haraji 
  • Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan
  • Ranar Maleriya Ta Duniya: ‘Yan Nijeriya Na Kashe Naira Tiriliyan 1.156 Duk Shekara Wajen Sayen Magunguna
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe