Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: 24th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda sun amince su dakatar da faɗa a gabashin ƙasar har sai an kammala tattaunawar sulhu da ke gudana a halin yanzu wanda Qatar ke shiga tsakani.
Wannan dai ita ce yarjejeniyar sulhu ta baya-bayan nan tun bayan da ƴan tawayen suka ƙara kai farmaki a gabashin ƙasar inda hukumomi suka ce an kashe mutane 7,000 tun daga watan Janairu.
A ranar Larabar da ta gabata ce, ɓangarorin biyu suka ba da sanarwar yin aiki tare don samar da zaman lafiya, bayan shafe sama da mako guda suna tattaunawa, wanda suka ce an gudanar cikin aminci tare da mutunta juna.
A watan da ya gabata, shugaban ƙasar Congo Félix Tshisekedi da takwaransa na Rwanda Paul Kagame suma sun jaddada aniyarsu ta tsagaita wuta ba tare da sharaɗi ba a wata ganawar ba-zata da suka yi a birnin Doha.
Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana gwabzawa ya ƙara kamari ne a watan Janairu, lokacin da ƙungiyar M23 ta ƙaddamar da wani farmaki da ba a taɓa ganin irinsa ba, inda ta ƙwace garuruwan Goma da Bukavu – manyan biranen ƙasar Congo guda biyu, lamarin da ya haifar da fargabar ɓarkewar yaƙi yankin baki ɗaya.
DR Congo na zargin Rwanda da bai wa ƙungiyar M23 makamai tare da tura dakaru domin tallafawa ƴan tawayen.
Duk da ikirarin da Majalisar Dinkin Duniya da Amurka suka yi, Rwanda ta musanta zargin da ake yi ma ta na goyon bayan ƙungiyar M23.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
Idan ka duba tarihin duniya gabadaya da tarihin annabawa, tarihi ne na wayewar duniya tun daga Annabi Nuhu (S.A.) har zuwa Manzon Allah (S.A.W.) kamar duniya tana ‘yar makaranta ce ta fara da Nazare, ta zo Firamare zuwa Sakandire har zuwa Jami’a, sannan aka yaye ta, yanzu da zuwan Manzon Allah an yaye duniya, yanzu duniya ba ta bukatar sai an aiko annabi, ba ta bukata sai an aiko ma’aiki, a’a wanna abu da Manzon Allah ya zo da shi za mu iya kafa dalili da shi mu shirya kanmu ba sai da annabi ba.
Wannan abu da Manzon Allah ya zo da shi yanzu ya kafa dalili da shi, da shi muka karantar da kanmu ba sai da Annabi ba, wannan abu da ya zo da shi za mu iya aiki da shi mu zauna lafiya, mu haramta abin da Allah Ya haramta. Yanzu kamar an yaye mu ne daga Jami’a tun daga jami’a tun daga zamanin Annabi Nuhu (A.S.) har ya zuwa Annabi Muhammadu (S.A.W.). idan ka faro duniya daga farkon ma’aika, duniya ta faro ne daga sanin wuta wato yadda za a yi amfani da wuta. Dan adam na farko ya ji tsoron wuta wasu sun tafi a kan cewa farkon abin da Dan Adam ya fara bautawa shine wuta, wanda ita ta fara ba shi tsoro ba wai ya iya kunnawa ba amma ya ga daki ya kama da wuta, dubi irin zamanin nan duk da motocin kashe gobara haka daji zai kama da wuta ta gagare su balle ka koma zamani da shekara miliyan kaza wanda dan Adam bai ma santa ba sai dai ya ga daki ya kama da wuta (wata ay ana cewa) “Allahn da ya sa muku wuta a ciki koren ganye ko koriyar bishiya”, malamai na cewa bishiya mai yado wanda ake kunna wuta, toh wannan abu ne ya sa idan wuta ta kama aka kasa shawo kanta sai mutane su tsorata su ce wai meye wannan, meye ya kunna wannan wutar? Suka ga to lallai wannan duniyar da suke ciki akwai wani abu a boye, gwara su bauta wa abin nan na boye fa, don ya kiyaye su daga wanna wutar har suka fara bauta mata da yanka dabbbobi don ta kiyaye su, gaba daya dai har ta soma gasa wasu abubuwa na dabbobi, idan wutar ta mutu suka zo wurin su ji kamshin ya bambanta, idan sun sa a baki su ji dadinsu ya banbanta. Toh tana daya daga cikin abin da ta koya wa dan Adam wayewa.
Da dan Adam ya waye, wuta tana daya daga cikin abin da ya wayar da dan Adam kuma idan ka lura yau wuta ita ke biye da mu duk wasu kere-kere za ka ga daga wuta ne, abin da muke tsoro kuma shi ne babban abin amfani, toh a haka dai dan Adam har ya iya kera wutar da kansa. Kamar yadda Allah ya fada mana cikin ‘ya’yan Adam da daya ya kashe daya ya rasa yadda zai yi, a haka ne har dan Adam ya san yadda zai binne dan’uwansa har zuwa zamanin Annabi Idirisu sama ta soma magana da kasa, Allah ya soma aiko ma dan Adam da mala’ika, su ne wadannan mutane da muke cewa ko akwai su a duniyar wata ko mutanen sama, Turawa duk sun rubuta wannan abu, sun zana wannan abu sai ga shi irin wannan jirage ne wanda ake cewa na duniyar sama, daya daga ciki Annabi Sha’ayahu yake cewa ga wani abu ya sauko kasa mai kara iri kaza.
Tun daga zamanin Annabi Idris mala’iku ne suka kawo sako suke yin magana da mutanen kasa, su ake cewa tatsuniyoyi na duk al’umma, tatsuniya ne a wajenmu amma su gaske ne a wajensu, su ce mutane sun sauko musu daga sama, har aka zo zamanin Annabi Nuhu ya tabbatar, da ya zo ya fada wa mutane suka ce ba su yarda ba, ba mu ji wannan wajen iyayenmu ba, haka aka ci gaba har zuwa zamanin Annabi Hudu dan Adam ya fara hore dabbobi, dabbar da dan Adam ya fara horewa shi ne kare, kuma ya hore dabbobin da zai ci, zai iya gane wannan dabbar ba zai ci ba wannan zai ci, wannan zai iya zama da ita lafiya, wannan ba zai iya zama da ita ba, daga nan dan Adam ya fara gini, ya dan kwakule kasa ya yi kogo ya shiga.
Har ya zuwa Annabi Salihu, har dan Adam ya fara fahimtar wannan kwayar da take fitowa a kasa, wannan zan iya ci in rayu, wannan kwayar kuma ba a cin ta, har ya soma tunanin toh wannan kwayar ya zan ajiye ta zuwa nan gaba in sake shuka ta, haka dan Adam har ya soma yin noma a aikace don ya rayu. Allah ya gaya mana wannan yana daga cikin ayoyin Allah (kamar yadda ya zo a aya) “arziki yana daga cikin kasa da abin da kasa take tsirarwa da abin da hannunka yake aikatawa” kamar sana’a ko noma ko nema. Toh ka ga a nan babu zancen ka ce ba za ka yi nema ba, duk abin da kake nema idan ka juya kasa za ka same shi, duka kasar da ta rike noma da sana’a za ku ga sun fi arziki, Allah ga shi ya gaya mana idan kafiri ya fi ka arziki sai dai ka nema a wajensa, don haka mu dogara da Allah shi ke azurtawa, ga ka’idoji nan ya fada mana, nema, kiwo abubuwa duk gabaki daya.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allahu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA