Kasar Yemen ta sanar da cewa: Amurka ta kaddamar da sabbin hare-haren wuce gona da iri kan garuruwan Sana’a, Sa’dah, da Al-Jawf

Mahukuntan Yemen sun sanar da cewa: Amurka ta ci gaba da kai hare-hare kan kasar Yemen, inda ta kaddamar da wasu jerin hare-hare kan garuruwan Sana’a, Sa’dah da Al-Jawf.

Wakilin Al-Alam ya ruwaito a yammacin jiya Juma’a cewa: Jiragen saman yakin Amurka sun kaddamar da hare-hare har sau shida a gundumar Bani Hushaysh dake arewa maso gabashin birnin Sana’a fadar mulkin kasar Yemen, inda suka yi luguden wuta a wurare da dama.

A lardin Al-Jawf, an kai wasu hare-hare 4 ta sama a gundumar Bart Al Anan da yankin Al-Yatmah da ke gundumar Khab da gundumar Al Sha’af a arewa maso gabashin kasar Yemen.

A ranar alhamis din da ta gabata, rundunar kawancen da Amurka ke jagoranta ta kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan birnin Al-Hodeida, inda suka yi ta kisan kiyashi kan fararen hula da ma’aikata a tashar Ra’as Issa da ke birnin. Hare-hare 14 ne suka kai kan cibiyoyin tashar jiragen ruwa da tankunan mai da iskar gas, inda suka kashe fararen hula fiye da 80 tare da raunata wasu 160, bisa ga kididdigar farko, a cewar ma’aikatar lafiya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ta kaddamar da

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura

Shugaban Ƙasar Gambiya, Adama Barrow, tare da matarsa Fatoumata Barrow, sun ziyarci Jihar Katsina, inda suka yi ta’aziyyar rasuwar tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari.

Sun kai ziyarar ne a ranar Juma’a domin jajanta wa iyalan marigayin game da rashin da suka yi.

Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar

Sun sauka a filin jirgin sama na Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, inda Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Barista Abdullahi Faskari, ya tarbe su a madadin Gwamna Dikko Umar Radda.

Bayan sojoji sun yi wa Shugaba Barrow faretin ban girma, sun wuce Daura kai-tsaye, inda suka yi wa iyalan marigayin da kuma Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk ta’aziyya.

 

Ga hotunan a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
  • Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar
  • HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
  • Robert Malley: Harin Amurka A Kan Wuraren Nukiliyar Iran Babban Kure Ne
  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing