Aminiya:
2025-05-01@04:40:00 GMT

Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas

Published: 16th, April 2025 GMT

Kwamitin wucin-gadi na Majalisar Wakilan Nijeriya wanda aka ɗora wa alhakin kula da harkokin gudanar da mulki a Jihar Ribas, ya gayyaci gwamnan riƙon jihar, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas.

Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Majalisar Wakilan, Akin Rotimi ya fitar a ranar Laraba.

An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato

Rotimi ya ce gayyatar na zuwa ne bayan ƙaddamar da kwamitin da Shugaban Majalisar Abbas Tajudeen ya yi a ranar Talata.

Ya ce gayyatar za ta bai wa kwamitin damar yin bita kan yadda al’amura ke gudana tun bayan kama ragamar aiki da Ibas ya yi a matsayin gwamnan riƙo a jihar ta Ribas.

Gayyatar wadda tuni ake aike da ita a hukumance, ta yi daidai da wasu tanade-tanade na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, inda ta buƙaci Ibas ya bayyana a gaban kwamitin da misalin ƙarfe 4 na maraicen ranar Alhamis, 17 ga watan Afrilun 2025.

A jiya Talata ce Majalisar Wakilan ta kafa tare da rantsar da kwamitin da zai kula da harkokin mulki a Jihar Ribas.

Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ya ce kwamitin na wucin gadi mai mamba 21 zai yi aiki kai-tsaye da gwamnan riƙo “kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya tanada.”

Majalisar ta kafa kwamatin ne bayan Shugaba Bola Tinubu ya saka dokar ta-ɓaci wadda ta dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar saboda abin da ya kira “rushewar doka da oda.”

Har yanzu dai ’yan adawa na zargin cewa Tinubu ya kafa dokar ne saboda rikicin siyasar da gwamnan na jam’’yyar PDP mai adawa yake yi da Ministan Abuja, Nyesom Wike, wanda ke ɗasawa da gwamnatin Tinubu ta APC.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Majalisar Wakilai Vice Admiral Ibok ete Ibas kwamitin da

এছাড়াও পড়ুন:

Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i

Kakakin kwamitin tsaron kasa a majalisar shawarar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; ” Ya zuwa yanzu ba za mu iya yin hukunci akan dalilan da su ka haddasa fashewar abubuwa a tashar ruwa ta Shahid Raja’i ba, amma za mu iya cewa babu hannu waje a ciki.

Kakakin kwamitin tsaron kasar ta Iran Ibrahim Rizai wanda ya halarci taron da aka yi a Majalisa akan fashewar da aka samu a tashar ruwan ta shahid Raja’i, ya kuma kara da cewa; Fahimtata da abinda na ji daga abokan aikina dangane da abinda ya faru a tashar ruwa ta Shahid Raja’i, da kuma rahotannin da su ka iso mana, shi ne cewa abinda ya farun ba shi da alaka da waje.”

 A ranar Asabar da ta gabata ne dai wasu abubuwa su ka fashe a tashar ruwa ta Shahid Raja’i dake Bandar Abbas a kudancin Iran, wanda ya haddasa asarar rayuka da kuma jikkatar daruruwan mutane.

An bude kwamitin bincike domin gano hakikanin abinda ya faru a tashar da kuma haddas fashewar abubuwan masu karfi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu