Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
Published: 9th, April 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin samar da kungiyar masu amfani da ruwan sha da makamantan su na 2025 ya zama doka.
Kudirin wanda zai bunkasa samar da ruwan sha da amfani a fadin jihar, ya samu karbuwa da amincewa cikin gaggawa saboda muhimmancin ruwa ga rayuwar al’umma.
Shugaban majalisar dokoki ta jihar, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudiring a lokacin zaman majalisar a Kaduna.
Kudirin da bangaren zartarwa na jihar ya aike da shi majalisar, an mika shi ga kwamitin ayyukan al’umma da samar da ababen more rdayuwa domin yin nazari akai, inda daga bisani ‘yan kwamitin suka tuntubi masu ruwa da tsaki a bangaren domin jin ba’asin su, sannan ya gabatar da bayanan da ya tattara da kuma shawarwari a zauren majalisar.
Shugaban kwamitin ayyukan al’umma da ababen more rayuwa, Alhaji Nasir Idris ya yi bayanin alfanun kudirin wajen bunkasa albarkatun ruwa a jihar da ma kasa baki daya.
Alhaji Nasir Idris ya lura cewa an amince da kudirin ne cikin hanzari duba da muhimmancin ruwa, wanda ya kasance wajen inganta lafiyar al’umma da zamantakewar su a jihar.
A wani labarin kuma, majalisar dokoki ta jihar Kaduna ta karba tare da amince da rahoton korafin da aka gabatar mata akan wani dan kwangila da aka baiwa aikin gina kasuwar Tudun Saibu ta Zamani a karamar hokumar Soba ta Jihar.
Da yake gabatar da rahoton binciken, Shugaban kwamitin bunkasa kasuwanni kuma dan majalisar mai wakiltar mazabar Jama’a, Mr. Ali Kalat aikin hadin gwiwa ne tsakanin majalisar karamar hukumar soba da wani kamfani Bebeji Integrated Services Limited wanda dan kwangilar ya gaza cika alkawarin da aka yi da shi,
A cewar rahoton, an kulla yarjejeniyar ce tun a watan Afrilun 2021 sannan a na sa ran kammalawa cikin kwanaki 90, sai dai dan kwangilar ya rushe gine-ginen tsohuwar kasuwar ce kawai ba tare da aza harsashin gina wata ba, duk da ikirarin da ya yi na cewa ya kai bulo 30,000 da siminti rabin tirela.
Kwamitin ya gano dan kwangilar ya saba yarjejeniya sannan ya bada shawarar a soke kwangilar domin a ba wani da ya cancanta domin gudanar da aikin.
Daga karshe kafatalin ‘yan majalisar sun amince da rahoton da kuma shawarwarin kwamitin.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: kasuwa Kungiyar Ruwan Sha
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.
A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.
Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.