Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin samar da kungiyar masu amfani da ruwan sha da makamantan su na 2025 ya zama doka.

Kudirin wanda zai bunkasa samar da ruwan sha da amfani a fadin jihar, ya samu karbuwa da amincewa cikin gaggawa saboda muhimmancin ruwa ga rayuwar al’umma.

Shugaban majalisar dokoki ta jihar, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudiring a lokacin zaman majalisar a Kaduna.

Kudirin da bangaren zartarwa na jihar ya aike da shi majalisar, an mika shi ga kwamitin ayyukan al’umma da samar da ababen more rdayuwa domin yin nazari akai, inda daga bisani ‘yan kwamitin suka tuntubi masu ruwa da tsaki a bangaren domin jin ba’asin su, sannan ya gabatar da bayanan da ya tattara da kuma shawarwari a zauren majalisar.

Shugaban kwamitin ayyukan al’umma da ababen more rayuwa, Alhaji Nasir Idris ya yi bayanin alfanun kudirin wajen bunkasa albarkatun ruwa a jihar da ma kasa baki daya.

Alhaji Nasir Idris ya lura cewa an amince da kudirin ne cikin hanzari duba da muhimmancin ruwa, wanda ya kasance wajen inganta lafiyar al’umma da zamantakewar su a jihar.

A wani labarin kuma, majalisar dokoki ta jihar Kaduna ta karba tare da amince da rahoton korafin da aka gabatar mata akan wani dan kwangila da aka baiwa aikin gina kasuwar Tudun Saibu ta Zamani a karamar hokumar Soba ta Jihar.

Da yake gabatar da rahoton binciken, Shugaban kwamitin bunkasa kasuwanni kuma dan majalisar mai wakiltar mazabar Jama’a, Mr. Ali Kalat aikin hadin gwiwa ne tsakanin majalisar karamar hukumar soba da wani kamfani Bebeji Integrated Services Limited wanda dan kwangilar ya gaza cika alkawarin da aka yi da shi,

A cewar rahoton, an kulla yarjejeniyar ce tun a watan Afrilun 2021 sannan a na sa ran kammalawa cikin kwanaki 90, sai dai dan kwangilar ya rushe gine-ginen tsohuwar kasuwar ce kawai ba tare da aza harsashin gina wata ba, duk da ikirarin da ya yi na cewa ya kai bulo 30,000 da siminti rabin tirela.

Kwamitin ya gano dan kwangilar ya saba yarjejeniya sannan ya bada shawarar a soke kwangilar domin a ba wani da ya cancanta domin gudanar da aikin.

Daga karshe kafatalin ‘yan majalisar sun amince da rahoton da kuma shawarwarin kwamitin.

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: kasuwa Kungiyar Ruwan Sha

এছাড়াও পড়ুন:

 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai

Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.

A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.

Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi