HausaTv:
2025-09-18@02:40:10 GMT

Amurka ta kai sabbin hare-hare 22 a kan Yemen

Published: 9th, April 2025 GMT

Amurka ta kai sabbin munanan hare-hare ta sama har sau 22 a wasu larduna da dama na kasar Yemen, jim kadan bayan kai wa kasar hare-hare da dama makamancin haka.

A cewar majiyoyin na Yemen, wadannan sabbin hare-hare na Amurka sun auna yankuna daban-daban a ranar Laraba, ciki har da babban birnin kasar Sanaa da lardin Ibb da ke tsakiyar kasar.

A Sana’a, an kai hare-hare ta sama guda takwas. Har yanzu ba a tabbatar da asarar rayuka ba, amma hare-haren sun shafi muhimman ababen more rayuwa, lamarin da ke kara tabarbare yanayin rayuwa ga fararen hula.

An sami adadin wadanda suka mutu mafi muni a lardin al-Hudaydah da ke yammacin kasar, inda aka tabbatar da mutuwar fararen hula 6 da suka hada da yara biyu da mace daya.

Akalla wasu mutane 16 sun jikkata, wadanda da dama daga cikinsu na cikin mawuyacin hali.

Da wadannan hare-hare, jimillar hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen ya kai 50 cikin sa’o’i 24 kacal.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar