Sai dai ya koka da yadda hare-haren da aka kai kwanan nan, inda aka tarwatsa sansanonin sojoji a Wajirko, Sabon Gari a karamar hukumar Damboa, Wulgo a Gamboru Ngala, Izge a karamar hukumar Gwoza da sauransu wanda hakan ya yi sanadin kashe mutane ‘yan gari da jami’an tsaro, lallai abun damuwa ne matuka.

 

Gwamna Zulum ya bayyana haka ne a wani taro na musamman na tsaro wanda ya samu halartar babban kwamandan runduna ta 7 ta rundunar sojojin Nijeriya, Manjo Janar Abubakar Haruna da kwamandojin sassan rundunar da kwamishinan ‘yansanda na jihar da shugabannin sauran hukumomin tsaro.

 

Taron ya kuma samu halartar Shehun Borno Alh. Dr. Abubakar Garbai Al-Amin El-Kanemi; Shehun Bama, Sarakunan Biu, Uba, Askira, Gwoza, yayin da Shehun Dikwa da Sarkin Shani aka wakilce su.

 

Zulum ya yabawa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da jami’an tsaro bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen yaki da Boko Haram.

 

Ya kara da cewa, dole ne a kara kaimi ta hanyar samar da kayan yaki na zamani ga sojoji domin dakile duk wani sabon harin da zai addabi sassan yankin Sahel na Borno da ke kan iyaka da kasashen Jamhuriyar Chadi, Nijar da Kamaru.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Ra’ayoyi daga sassan kasa da kasa sun karkata ga muhimmancin taron kolin ASEAN-Sin-GCC karo na farko da ya gudana a birnin Kuala Lumpur fadar mulkin kasar Malaysia a jiya Talata 27 ga watan nan.

Daga mahanga ta shiyya, taron bangarorin uku ya mayar da hankali ga manyan sassa uku, wadanda suka hada da gabashin Asiya, da kudu maso gabashin Asiya da yankin Middle East, tare da cewa ba kasafai ake samun irin wannan hadin gwiwar shiyyoyi a yankin Asiya ba.

A gabar da ake fuskantar tarin kalubale a matakin kasa da kasa masu matukar sarkakiya, da raunin bunkasar tattalin arzikin duniya, Sin da ASEAN da GCC na aiki tare domin gina da’irar tattalin arziki ta bai daya da ci gaba tare. Hakan ba kawai zai amfani tattalin arzikin sassan ba ne, har ma zai ingiza yanayin zaman lafiya, da ci gaba a Asiya da ma sauran sassan duniya baki daya.

Sin da kasashe mambobin ASEAN, da na GCC dukkanin su suna da muhimmanci cikin jerin kasashe masu tasowa. Wannan taron koli na hadakar sassa uku ya mayar da hankali ga zakulo sabon tsarin hadin gwiwar shiyyoyi tsakanin kasashe masu tasowa, wanda hakan ke da matukar muhimmanci. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci
  • HKI Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’a
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno
  • Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
  • Rundunar Ƴansanda Ta Gayyaci Jami’anta Da Bidiyonu Ya Yaɗu Suna Karɓar Cin Hancin Naira 5000
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu
  • Gwamnatin Sudan Ta Yi Allah Wadai Da Sabbin Takunkuman Da Amurka Ta Kakaba Mata