HausaTv:
2025-09-18@05:27:20 GMT

Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan Yemen

Published: 7th, April 2025 GMT

Amurka na ci gaba da kai hare-hare kan Yemen, inda ta kai sabbin hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar a baya bayan nan.

Kafar yada labaran kasar Yemen ta bayyana cewa, Amurka ta kai akalla hare-haren jiragen yaki guda uku a gundumar Bani Matar da ke lardin Sanaa.

Akalla fararen hula hudu ne suka mutu sannan wasu 25 suka jikkata, ciki har da mata 11 da yaro daya.

Hakazalika jiragen yakin Amurka sun kai hare-hare guda hudu a tsibirin Kamaran da ke al-Hudaydah a yammacin kasar Yemen.

Wasu hare-hare uku na Amurka sun kai hari a lardin Hajjah da ke yammacin kasar Yemen.

Amurka da kawayenta sun zafafa kai hare-hare kan kasar Yemen bayan da ta koma yaki da Isra’ila sakamakon sabon kisan kiyashi da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza.

Galibin hare-haren da Amurka ke kaiwa kan gine-ginen fararen hula ne, lamarin da ke haddasa mace-mace da jikkata a tsakanin jama’a.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har kullum, Sin za ta ci gaba da martaba ka’idojin kare hakkokin kamfanoninta. Duba da cewa manhajar TikTok ta shafe tsawon shekaru tana aiki a Amurka, ta kuma samar da dumbin ayyukan yi ga tarin Amurkawa, tare da bayar da gudummawa ga tattalin arzikin kasar, ya kamata gwamnatin kasar ta baiwa manhajar damar cin gajiya daidai da sauran makamantanta dake kasar. Kamar dai ko da yaushe, burin Sin shi ne wanzar da daidaito da cimma moriyar bai daya tare da Amurka.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar