HausaTv:
2025-08-01@15:11:28 GMT

Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan Yemen

Published: 7th, April 2025 GMT

Amurka na ci gaba da kai hare-hare kan Yemen, inda ta kai sabbin hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar a baya bayan nan.

Kafar yada labaran kasar Yemen ta bayyana cewa, Amurka ta kai akalla hare-haren jiragen yaki guda uku a gundumar Bani Matar da ke lardin Sanaa.

Akalla fararen hula hudu ne suka mutu sannan wasu 25 suka jikkata, ciki har da mata 11 da yaro daya.

Hakazalika jiragen yakin Amurka sun kai hare-hare guda hudu a tsibirin Kamaran da ke al-Hudaydah a yammacin kasar Yemen.

Wasu hare-hare uku na Amurka sun kai hari a lardin Hajjah da ke yammacin kasar Yemen.

Amurka da kawayenta sun zafafa kai hare-hare kan kasar Yemen bayan da ta koma yaki da Isra’ila sakamakon sabon kisan kiyashi da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza.

Galibin hare-haren da Amurka ke kaiwa kan gine-ginen fararen hula ne, lamarin da ke haddasa mace-mace da jikkata a tsakanin jama’a.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu kasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban kasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alakar tarihi tsakanin kasar Laberiya da Amurka. Bugu da kari, Trump ya katse maganar shugaban kasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri. A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar—ba domin neman karfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka din damar samun ma’adanan da take bukata, da yiwuwar sanya wadannan kasashen dake nahiyar Afirka amincewa da karbar bakin haure da ake korarsu daga Amurka.

Watakila, shugaba Trump ba ya mai da hankali sosai kan da’a a fannin diflomasiyya, amma idan aka kwatanta da shugabannin kasar Amurka da suka gabace shi, to, a kalla yana bayyana kome a fili ba tare da rufa-rufa ba. Maganarsa da matakan da ya dauka, dukkansu na isar da sako zuwa ga kasashen Afirka cewa: “Ba ku cikin jerin fannonin da Amurka take nunawa fifiko.” “Za mu iya musayar wasu abubuwa, amma kada ku yi tsammanin za ku samu riba ko alfanu sosai.” (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami