Aminiya:
2025-04-30@19:48:19 GMT

Turji ya kusa komawa ga mahallici –  Sojoji

Published: 4th, April 2025 GMT

A ranar Alhamis ɗin nan ne rundunar sojin Nijeriya ta ce ana cigaba da farautar  ƙasurgumin ɗanbindiga, Kachalla Bello Turji wanda sojojin ƙasar suka daɗe suna nema ya kusa komawa ga mahalicci.

Rundunar ta bayyana cewa kuma kwanakinsa sun kusa ƙarewa.

Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta miƙa Janar Tsiga da wasu ga NSA Gobara ta tashi a Jami’ar Northwest da ke Kano

Ta kuma yi watsi da iƙirarin da ake na cewa sojoji sun rage kai hare-hare kan makiyaya, ’yan bindiga, ɓarayin shanu da sauransu, inda ta ƙara da cewa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen kame Turji.

Wannan na zuwa ne kimanin kwana ɗaya bayan Turji ya kashe manoma 11 a garin Lugu da ke ƙaramar Isa ta Jihar Sokoto

An samu rahoton Turji yana dawowa ne daga ziyarar Sallah da ya kai wata unguwa a Isa, lokacin da ya kai harin.

Da yake amsa tambayoyi daga ‘yan jarida a hedikwatar tsaro a yayin ganawa da manema labarai, daraktan watsa labaran na rundunar tsaro ta Najeriya, Manjo Janar Markus Kangye, ya ce za su iya ci gaba da farauta tare da ganin bayan manyan ’yan bindiga da ke cikin dazukan ƙasar nan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rundunar Sojoji

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi