Turji ya kusa komawa ga mahallici – Sojoji
Published: 4th, April 2025 GMT
A ranar Alhamis ɗin nan ne rundunar sojin Nijeriya ta ce ana cigaba da farautar ƙasurgumin ɗanbindiga, Kachalla Bello Turji wanda sojojin ƙasar suka daɗe suna nema ya kusa komawa ga mahalicci.
Rundunar ta bayyana cewa kuma kwanakinsa sun kusa ƙarewa.
Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta miƙa Janar Tsiga da wasu ga NSA Gobara ta tashi a Jami’ar Northwest da ke KanoTa kuma yi watsi da iƙirarin da ake na cewa sojoji sun rage kai hare-hare kan makiyaya, ’yan bindiga, ɓarayin shanu da sauransu, inda ta ƙara da cewa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen kame Turji.
Wannan na zuwa ne kimanin kwana ɗaya bayan Turji ya kashe manoma 11 a garin Lugu da ke ƙaramar Isa ta Jihar Sokoto
An samu rahoton Turji yana dawowa ne daga ziyarar Sallah da ya kai wata unguwa a Isa, lokacin da ya kai harin.
Da yake amsa tambayoyi daga ‘yan jarida a hedikwatar tsaro a yayin ganawa da manema labarai, daraktan watsa labaran na rundunar tsaro ta Najeriya, Manjo Janar Markus Kangye, ya ce za su iya ci gaba da farauta tare da ganin bayan manyan ’yan bindiga da ke cikin dazukan ƙasar nan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rundunar Sojoji
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
A yau Alhamis ne aka bude bikin baje kolin hada-hadar tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan, taron dake kara jaddada himmar kasar Sin ta fuskar karfafa alaka da nahiyar Afirka, nahiyar dake da mafiya yawan kasashe masu tasowa a duniya baki daya.
Kusan kamfanonin Sin da na kasashen Afirka 4,700, da sama da mahalarta 30,000 ne za su halarci bikin na kwanaki hudu, wanda aka yiwa taken “Sin da Afirka: Tunkarar zamanantarwa tare.” Rahotanni daga mashirya bikin na cewa, kwarya-kwaryar darajar ayyukan hadin gwiwa da aka amincewa sun haura dalar Amurka biliyan 11.
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin bude baje kolin, inda kuma ya yi amannar cewa taron zai samar da karin damammaki ga hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da haifar da kyakkyawan sakamako.
Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya kara da cewa, duk irin sauyin da aka samu a fannin cudanyar sassan kasa da kasa, Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da nahiyar Afirka, za ta samar da kakkarfan tallafi ga ayyukan zamanantar da nahiyar, da kasancewa kawa ta gari, kuma sahihiyar ‘yar uwa ga Afirka kan hanyar nahiyar ta samun ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp