Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II ya ce duk wani mai ƙoƙarin ja da hukuncin Allah to ba zai taba wanyewa lafiya ba.

Sanusi II ya ce duk wani mai ƙoƙarin kawo tazgaro ga zaman lafiyar Jihar Kano a ƙarshe aniyyarsa ce za ta koma kansa.

SSarkin ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan rediyon Premier da ke Kano, inda yake roƙon al’ummar jihar su zamo masu bin doka da oda, da kuma gudun aikata abubuwan da ka iya ta da hankali.

Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe

Kazalika ya bayyana masu ƙalubalantar kasancewarsa Sarki a matsayin masu yaƙi da nufin Allah, kuma a cewarsa hakan ba zai taɓa zame musu alheri ba.

Da yake jan hankalin Kanawan kan muhimmancin haƙuri da addu’a a wannan gaɓar, Sarkin ya ce turka-turkar da ake ciki game da masarautar Kano ba wai don shi ake yi ba, sai domin yaƙi da hukuncin Allah.

“Muna kira ga al’umma da su zamo masu bin doka da oda. Wannan rigimar ba da ni ake yinta ba, yaƙi ne da abinda Allah Ya ƙaddara.

“Ina roƙonku ku yi haƙuri ku dage da addu’a. Tabbas Allah Zai ci gaba da goya wa adalai baya.

“Wuta kuma ita ce karshen duk wani mai shirya wa Kano maƙarƙashiya. Allah Ya hana shi zaman lafiya.

“Muna roƙon Allah Ya kare kasarmu da rayukanmu. Da yardar Allah duk mai kokawa da hukuncin Allah ba zai gama da duniya lafiya ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Sarkin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027

’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.

Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Duk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).

Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.

Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.

“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.

Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.

Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.

“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.

Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.

A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.

Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.

Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.

“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.

Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?

Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.

“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.

“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.

Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.

Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.

Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.

Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.

Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.

“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano