HausaTv:
2025-04-28@19:14:40 GMT

Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum

Published: 21st, March 2025 GMT

Sojojin Sudan sun sanar a yau Juma’a cewa sun kwace iko da fadar shugaban kasa dake tsakiyar birnin Khartum, bayan da su ka kori mayakan rundunar kai daukin gaggawa.

Majiyar ta ce, sojojin na Sudan sun fara da kutsawa cikin fadar shugaban kasar ne, ta mashigar gabas,bayan da su ka kashe mayakan rundunar kai daukin gaggawa da dama,yayin da wasu da dama su ka gudu zuwa cikin kasuwar dake kusa.

Bayanin da sojojin na Sudan su ka fitar ya kunshi cewa; Mun murkushe mayakan Duqlu, ‘yan ta’adda a tsakiyar birnin Khartum da kuma kasuwar Larabawa da ginin fadar shugaban kasa da sauran ma’aikatu.”

Har ila yau majiyar sojan na Sudan ta ce,su kuma yi nasarar rusa makamai da motocin yakin rundunar kai daukin ggagawar,kamar kuma yadda ta kame wasu masu maya.

Janar Nabil Abdullah wanda shi ne kakakin sojan na Sudan ya sanar da cewa; Za su ci gaba kai hare-hare a cikin dukkanin fagagen yaki har samun nasara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ƙwato Bindigogi Da Tabar Wiwi A Zamfara Bayan Artabu Da ‘Yan Bindiga

Kwamishina CP Ibrahim Maikaba ya yaba da ƙoƙarin jami’ansa, yana kuma ƙara jaddada niyyar rundunar na yin aiki tare da al’umma domin samar da tsaro.

Ya buƙaci mutane su riƙa bai wa rundunar sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka.

Rundunar ta kuma fitar da lambobin da za a iya kira idan aka ga wani abu da ba a gamsu da shi ba; 08034805544, 07032490813 da kuma 09053872244

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa
  •  Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun kashe ‘Yan Hijira Da Dama A Yankin Tekun Maliya
  • Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  • An Kammala Jana’izar Paparoma Farancis A Birnin Vatican
  • Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG
  • ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
  • ‘Yansanda Sun Ƙwato Bindigogi Da Tabar Wiwi A Zamfara Bayan Artabu Da ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
  •  Kotun Tsarin Mulki Ta Gabon Ta Tabbatar Da Nasarar Nguema A Zaben Shugaban Kasa