Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM
Published: 12th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta umarci Babban Bankin Najeriya (CBN), da ya dakatar da sabon tsarin ƙarin caji kan cire kuɗi ta na’urorin ATM.
Wannan umarni ya biyo bayan wata sanarwa da CBN ya fitar, inda ya ƙuduri aniyar fara cajin Naira 100 kan duk cire Naira 20,000 daga ATM a banki, daga ranar 1 ga watan Maris, 2025.
Ɗan majalisa Marcus Onobun (PDP, Edo) ne, ya jagoranci ƙudirin da ya buƙaci a dakatar da wannan tsari, inda ya bayyana cewa tsarin zai ƙara jefa ’yan Najeriya cikin wahala.
Ya bayyana cewa, a shekarar 2019, an rage cajin cire kuɗi ta ATM daga Naira 65 zuwa Naira 35, don sauƙaƙa wa al’umma.
Sabon tsarin na CBN ya tanadi cewa, idan kwastoma ya cire kuɗi daga ATM na bankinsa, ba za a caje shi komai ba; amma idan ya cire daga ATM na wani banki daban, za a caje shi Naira 100 kan kowace Naira 20,000 da ya cire.
Majalisar ta nuna damuwa cewa wannan ƙarin caji zai ƙara matsin lamba ga ‘yan Najeriya, musamman ma masu ƙaramin ƙarfi, waɗanda ke fama da hauhawar farashin kayayyaki da sauran matsalolin tattalin arziƙi.
Saboda haka, ta umarci CBN da ya dakatar da aiwatar da wannan sabon tsari har sai an gudanar da cikakken nazari tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin samun mafita mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Sabon Tsari a dakatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.