Aminiya:
2025-08-01@20:53:04 GMT

Burina in yi fice kamar mahaifiyata — Maryam ‘Yar Auta

Published: 2nd, March 2025 GMT

Maryam Abubakar sabuwar jaruma ce a Masana’antar Kannywood ’yar Hajiya Hauwa Garba da aka fi sani da ’Yar Auta ko Sabirar Gidan Badamasi.

A zantawarta da Aminiya ta ce babban burinta shi ne ta yi fice da suna kamar yadda mahaifiyarta Hajiya Hauwa Garba ta yi:

Mene ne takaitaccen tarihinki?

Sunana Maryam Abubakar wadda aka fi sani da Maryam Intete.

An haife ni a Najeriya na yi makarantar firamare a Kawo (Kawo ta Kano), na yi karamar sakandare a Jogana, na kuma yi makarantar Unguwar Badawa a matakin Babbar Sakandare daga nan sai na tafi Saudiyya, inda a can na kara karatu. Yanzu ina da shekara 22 a duniya.

Yaya aka yi kika tsinci kanki a Masana’antar Kannywood?

Eh, ina harkar fim yanzu kuma zan iya cewa ina cikin wadanda suka fara tunda kuruciyarsu.

Na taso na ga yadda mahaifiyata take yi ne, shi ya sa ni ma na ce ina da sha’awar shiga harkar don in bayar da tawa gudunmawar.

Wane buri kike da shi tun kina karama?

Insha Allah zan ci gaba da karatuna don yanzu haka ina kokari ci gaba da karatu domin kwarewa a wani fannin daban bayan fim.

Shin kin haɗu da wasu matsaloli da kika fara fim?

Gaskiya ban haɗu da wata matsala ba, don ina yin wasu ’yan abubuwa haka ina ɗora wa a shafina na TikTok, wasu na yi min magana suna cewa gara ki hakura da fim ki yi aure. Ni kuma sai in ce musu aure lokaci ne insha Allahu zan yi idan lokacin ya zo.

Waɗanne abubuwa kike ganin ba haka kika zata ba a Kannywood?

Gaskiya idan zan iya bayar da shawara, idan mutum bai iya abu ba, yana da kyau ka zaunar da shi ka fahimtar da shi ko kuma idan an kawo maka kushe misali a ce idan ka zauna da mutum ka ji mene ne dalili?

Kada ka yanke hukunci nan take ba tare da jin ta bakinsa ba. Yanke hukunci lokaci daya babu kyau.

Mu ’yan Adam ne muna saba wa junanmu wani abin ma ai ba ka yi ba sai a je wajen ubangidanka a ce ka yi wani abu alhali ba ka yi ba. To wannan ne gaskiya nake ba manyanmu shawara su rika jin ta bakinmu idan an kawo musu kushe.

Mene ne burinki a masana’antar?

Ina fatar abubuwa da yawa. Na farko ina so in ga na yi suna kamar yadda mahaifiyata Hajiya Hauwa Garba ta yi.

Na biyu ina so in shahara a duniyar fim baki ɗaya.

Wane fim kika fi son fitowa a ciki?

Yanzu ka ga da Chamama da Barkwanci duk sun haɗu ba a gane kowane ɓangaren.

Ina hadawa ne, amma ba na yin kwalliya irin ta mahaifiyata.

A cikin finafinan da kika fito, wanne ya fi burge ki?

Akalla dai na yi finafinai da dama, amma uku sun fi fice saboda ban dade ba a masana’antar. Amma a ciki wanda ya fi burge ni shi ne Naja’atu.

Wadanne nasarori kika samu?

AlhdulilLahi na samu nasarori da dama. A ce mutum ya yi fice a san shi ma ai wani abu ne.

Nasarata ta farko da na samu zuwa na aikin Saudiyya na ga mutane da yawa sun san ni da suka gan ni, na ji matukar farin cikin yadda suke nuna ni. Wannan kadai ma nasara ce.

Wasu za su so sanin dalilin da ya sa kika haɗa sana’a da mahaifiyarki?

Ban ga abin mamaki ba, saboda tun ina yarinya mahaifiyata take harkar fim, wanda hakan ya sa na saba ganin yadda take yi. Wannan ya sa ko da na shigo ban sha wahala ba.

Kin fuskanci ƙalubale ko turjiya ta wajen mahaifi kan wannan harka?

Eh, mahaifina da farko ya ce min ba ya son harkar fim, ya fi son in yi aure, amma da na zauna muka fahimci juna da shi sai ya ce min shi ke nan babu damuwa Allah Ya taimaka.

Sakonki ga masu bibiyar finafinanki da masoyanki?

To sakona gare su shi ne su ci gaba da yi min addu’a Ubangiji Allah Ya kai ni gabar da nake son kaiwa. Ina godiya gare su. Allah Ya bar zumunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hauwa Garba Maryam Abubakar

এছাড়াও পড়ুন:

Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.

Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.

Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.

“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.

“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.

Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.

“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”

Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba