Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki
Published: 28th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta buƙaci malaman jami’ar jihar da suka shiga yajin aiki da su koma bakin aiki don ci gaban ilimi a jihar.
Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Farfesa Isah Muhammad Maishanu ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, kwana ɗaya bayan da malaman suka fara yajin aiki saboda rashin biyansu haƙƙoƙinsu.
Ya ce: “Muna kira ga malaman da su sake tunani kan matakin da suka dauka. Kada su bari siyasa ko wasu da ba su da kishin jiha su yi amfani da su wajen hana ci gaban ilimi.
“Mu na mutunta su, kuma muna fatan su koma bakin aikinsu.”
Ya ƙara da cewa gwamnati ta ɗauki ƙorafe-ƙorafen malaman da muhimmanci, don haka an kafa kwamiti da ke tattaunawa da ɓangarorin da abin ya shafa kan matsalar rashin biyan su kaso 25 da 35 na albashinsu.
Dangane da matsalar gidajen malamai da suka fara lalacewa, kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta tura injiniyoyi domin tantance halin da suke ciki da nufin gyara su.
Duk da haka, wasu masu sharhi a Sakkwato na ganin cewa gwamnati ba ta ɗauki matakan da suka dace don warware matsalar malaman ba.
A cewarsu, maimakon ɗaukar matakin magance matsalolin, gwamnati kawai tana bayar da umarni ne wanda ba ya taimakawa wajen yin sulhu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA