2025-10-26@08:10:21 GMT
إجمالي نتائج البحث: 10716

«da Majalisar»:

    Dakarun rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) sun daƙile harin da ’yan ta’addan ISWAP suka kai a garin Gamborun Ngala da ke kan iyakar Najeriya da ƙasar Kamaru. Rahotanni daga rundunar sun nuna cewa an kai harin ne da misalin ƙarfe 6:15 na yammacin ranar Asabar, inda aka ji ƙarar harbe-harbe masu ƙarfi a sassa daban-daban na garin. ABU ta musanta zargin ƙera makamin nukiliya a ɓoye An ba da tallafin N2m ga iyalan jami’in NSCDC da aka kashe a Jigawa  Sai dai a cewar majiyoyi, sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, inda suka shiga fafatawa da ’yan ta’addan, kuma suka fatattake su ba tare da wata asara a ɓangaren dakarun ba. Wakilinmu ya ruwaito cewa babu wani soja ko...
    Gwamnatin Jihar Jigawa ta bayar da tallafin Naira miliyan biyu ga iyalan SC Bashir Adamu Jibrin, jami’in hukumar sibil difens (NSCDC) da ya rasu a bakin aiki a kasuwar Shuwarin da ke ƙaramar hukumar Kiyawa. Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, ne ya miƙa tallafin ga matar marigayin a ofishinsa, inda ya ce wannan taimako na nufin tallafa wa iyalan marigayin tare da taimaka musu wajen kula da tarbiyyar ’ya’yansu. Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum ABU ta musanta zargin ƙera makamin nukiliya a ɓoye Ya shawarci matar marigayin da ta yi amfani da kuɗaɗen wajen kula da ilimi da walwalar ’ya’yanta, tare da jaddada cewa gwamnatin Jigawa za ta ci gaba da...
    A gobe Litinin ne za a bude taron kungiyar tattalin arziki ta “Eco” a nan birnin Tehran,kamar yadda mataimakin ministan harkokin cikin gida na Iran Ali Zaini Wand ya sanar. Taron dai za a yi shi ne a matakin ministocin harkokin cikin gida domin Shata hanyoyin aiki a tare a tsakaninsu, bayan da aka dauki shekaru 15, ba a gudanar da shi ba. Ali Zaidani ya kuma yi ishara da cewa taron na wannan karon zai mayar da hankali ne akan hanyoyin bunkasa alaka da kasashen makwabta,musamma bisa la’akari da cewa gundumomin Iran da suke aka iyaka suna da kyakkyawar alaka da kasashen makwabta. Bugu da kari  taron na kungiyar “Eco” zai yi kokarin kawar da kalubalen da ake fuskata...
    Kafar watsa labaru ta “Afircanews” ta bayyana cewa, babu wani cikakken dalili da aka gabatar dangane da sauye-sauyen, tare da kuma kore jita-jitar da aka rika watsawa akan yunkurin juyin Mulki a kasar a watan Satumba, dda ya kai ga tsare sojoji 20 daga ciki har da Birgediya janar da kuma kanar. Mai Magana da yawun shugaban kasar ta Nigeria, ya bayyana cewa; shugaba Ahamd Tinubu ya salami manyan jami’an sojoji da su ka hada babban hafsan hafsoshi Emmanuel Ogalla, shugaban sojan ruwa, da Hassan Abubakar, shugaban sojan sama. Shugaba Ahmad Tinubu ya nada Olufemi Oluyedi, tsohon hafsan hafsoshin soja a matsayin sabon ministan tsaro.  Sabon shugaban sojan kasa shi ne Manjo janar W. Shaibu Shugaban sojan Sama kuma shi...
    Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran  Ali Larijani ya bayyana cewa; Bayan da aka dauki shekaru biyu ana yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi, wanda mutane 70,000 su ka yi shahada, wasu fiye da 100,000 su ka jikkata, suna son a rufe wannan laifin da taron zaman lafiya. Ali Larijani ya kara da cewa; Sun kashe al’ummar Falasdinu, sun hana shi abinci da ruwa, yanzu kuma suna son bayyana kawukansu a matsayin masu ceto da Falasdinawa, don haka wannan taron ba komai ba ne sai wasan kwaikwaiyo. Taron da aka yi a Sherm-Sheikh na Masar an yi shi ne a karkashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump wanda kasarsa ce ta kasance a gaba wajen bayar da makamai ga...
    Yana magana ko jawabi cikin hankali, amma kuma shawarwarin da yake badawa suna da matuƙar amfani wajen kawo gyaran wurare da dama. Mai ilimi, tsara yadda za’a ɓullo ma al’amura, mutunci ga kuma kwarjini da ƙwarewa An haife Kalu 5 ga Mayu, 1971, a Agbamuzu, a ƙaramar hukumar Bende ta Jihar Abia State, tarihin rayuwar Kalu ya fara ne daga aiki da kuma samun tallafin ƙaro ilimi. Yana da digirin digirgir PhD a tsarin al’umma da kuma karatun abinda da wayo ake koyonsa (Jami’ar Abuja), da kuma LL.M akan ta’addanci da taimakawa kan jin ƙai  (Distinction, daga Jami’ar Kalaba), da MBA daga Jami’ar Oɗford Brookes  (UK), da kuma LL.B (Hons.) daga Kalaba. Ya cigaba da karatu— halin yanzu yana karanta...
    A yau Asabar 25 ga wannan wata, ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar sun gudanar da liyafar murnar kebe ranar tunawa da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin Taiwan, a dakin taro na Diaoyutai dake birnin Beijing. Wakilan bangarori daban daban na yankin Taiwan da na babban yankin kasar Sin masu halartar bikin murnar cika shekaru 80 da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin Taiwan da safiyar wannan rana sun halarci liyafar. Direktan ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin da ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar...
    Wannan shi ne daya daga cikin martanin NASENI da abokan huldarta don samar da CNG, wannan kuma na daga shirin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na daƙile tasirin cire tallafin man fetur ta hanyar samar da iskar gas mai rahusa. Manufar ita ce a rage dogaro da na’urorin lantarki da ake shigowa da su daga waje, da inganta dogaro da kai a ɓangaren fasaha, da samar da ayyukan yi. NASENI tana ba da ababen more rayuwa da tallafin manufofin, yayin da ɓangaren da ke kula da masana’antu, yana mai da hankali kan haɗin gwiwa, ƙirƙira da kasuwanci don kafa Nijeriya a matsayin cibiyar fasahar Afirka. Wannan dabarar da NASENI ta yi ya tabbatar da cewa ba a bar kasar a baya...
    “Ban taba tunanin zan zama taurariya a duniya ba.” Daga Yobe Zuwa Fagen Duniya An haife ta a Jihar Kano kuma ta tashi a Yobe, labarin Nafisa ba shi da wuya kamar yadda yake da ban sha’awa. Mahaifinta ya rasu tun tana jaririya, kuma mijin mahaifiyarta mai suna Alhaji Yusuf Umar Kaigama ya rene ta, wanda ya dasa mata dabi’u na tarbiyya da azama. Tana kuma ɗauke da tsatson sarautar zuriyar sarakuna biyu masu daraja ta masarautar Kano, wato Sarkin Kano Ibrahim Dabo da Sarki Abdullahi Maje Karofi. Amma bayan jinin sarautar da take ɗauke dasu, yunwar ta na neman ilimi ya sa ta zama daban. A yanki da matsalar staro ta yi katutu wanda kuma yake dakushe duk wani...
    Wakilan kasar Sin da na Amurka sun yi taro da safiyar yau Asabar don tattaunawa kan batutuwan tattalin arziki da cinikayya. A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis da ta gabata, wani mai magana da yawun ma’aikatar harkokin kasuwanci ta kasar Sin, ya bayyana cewa, bangarorin biyu za su gudanar da shawarwari kan muhimman batutuwa game da huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, bisa muhimmiyar yarjejeniyar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin da suka tattauna ta wayar tarho a wannan shekarar. Mataimakin firaministan kasar Sin kuma memba na ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin He Lifeng ne ke jagorantar tawagar kasar ta Sin a tattaunawar. (Abdulrazaq Yahuza Jere)...
    Jami’ar Tarayya ta Dutsinma ta zabi Farfesa Muhammed Khalid Othman a matsayin sabon Shugaban Jami’ar na dindindin, tare da amincewar Majalisar Gudanarwar Jami’ar. Da yake zantawa da manema labarai a Dutse, babban birnin jihar Jigawa, Magatakardar Jami’ar, Dokta Musa Ajiya, ya bayyana cewa mai kula da jami’ar (Pro-Chancellor), Ali Abubakar-Jatau, ne ya sanar da nadin. A cewar Dokta Ajiya, Abubakar Jatau wanda shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa, ya bayyana hakan ne bayan taron na musamman karo na 36 da aka gudanar a daren Juma’a. Ya ce Farfesa Othman ya fito ne a matsayin wanda ya fi kowa cancanta bayan wani tsari na tantancewa mai tsauri kuma bisa gaskiya, a cikin mutane 17  da suka nemi mukamin 17. Ya ƙara da...
    Firaministan kasar Sin Li Qiang ya isa Singapore a yau Asabar don ziyarar aiki a kasar bisa gayyatar firaministan Singapore Lawrence Wong. Li ya bayyana cewa, a cikin shekaru 35 da suka gabata tun bayan kafa huldar diflomasiyya, dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ta ci gaba da kasancewa mai kyau da samun ci gaba, tare da zurfafa amincewa da juna a siyasance, da hadin gwiwa mai amfani da kuma mu’amala ta kut-da-kut tsakanin mutanensu, wanda ya kafa misali don koyo tare da hadin gwiwar samun nasara ga kowane bangare a tsakanin kasashe. Ya kara da cewa, kasar Sin tana son yin aiki tare da Singapore don karfafa daidaita dabarun ci gaba, da fadada hadin gwiwa mai amfani ga dukkan...
    Wannan shi ne daya daga cikin martanin NASENI da abokan huldarta don samar da CNG, wannan kuma na daga shirin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na daƙile tasirin cire tallafin man fetur ta hanyar samar da iskar gas mai rahusa. Manufar ita ce a rage dogaro da na’urorin lantarki da ake shigowa da su daga waje, da inganta dogaro da kai a ɓangaren fasaha, da samar da ayyukan yi. NASENI tana ba da ababen more rayuwa da tallafin manufofin, yayin da ɓangaren da ke kula da masana’antu, yana mai da hankali kan haɗin gwiwa, ƙirƙira da kasuwanci don kafa Nijeriya a matsayin cibiyar fasahar Afirka. Wannan dabarar da NASENI ta yi ya tabbatar da cewa ba a bar kasar a baya...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD October 25, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15 October 25, 2025 Daga Birnin Sin An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC October 25, 2025
    Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU,  ta ƙaryata labaran da ke yawo a kafafen sada zumunta, cewa tana aikin ƙera makamin nukiliya a ɓoye a cikin jami’ar. A wata sanarwa da ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na jami’ar, ƙarƙashin Malam Auwalu Umar, ya fitar, jami’ar ta bayyana cewa labaran da ake yaɗawa ba su da tushe balle makama. Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam “Mun lura da wani faifan bidiyo da na’urar AI ta ƙirƙira, wanda wasu ke yaɗawa suna iƙirarin cewa ABU na ƙera makamin nukiliya a ɓoye. Wannan ƙarya ce babu gaskiya a cikinta,” in ji...
    Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zaria, ta karyata wani faifan bidiyo da aka yada a kafafen sada zumunta da ke zargin cewa jami’ar na da hannu wajen wani shiri na sirri kan hada makamin nukiliya a Nijeriya. A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a na jami’ar, Malam Auwalu Umar, ya fitar a ranar Asabar, jami’ar ta bayyana cewa wannan faifan bidiyon da aka samar ta hanyar na’urar kirkirar bidiyo, karya ne kuma an shirya shi ne don rikita jama’a da bata hakikanin manufar kasar wajen amfani da makamashin nukiliya. Umar ya jaddada cewa dukkan aiyukan nukiliyar Nijeriya ana gudanar da su ne bisa tsarin lumana da kuma bin ka’idodin kasa da kasa kamar yarjejeniyar NPT da Pelindaba Treaty, wadda ta...
    Gungun kogiyoyin bada agaji sun yi gargadin cewa yanayin da rayuwar ke gudana a yankin gaza ya zarce yadda ake tsammani, duk da abin da aka kira da tsagaita wuta, kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana akalla falasdinawa 1.5 suka cikin bukatar gaggawa domin tsira da rayuwarsu. Duk da cika kwanaki 13 da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin Gaza tsakanin Hamas da isra’ila, amma alumma suna cikin bala’I a yankin, duk da gargadin da ake yi akan haka,  sama dai kungiyoyin agaji 41 ne suka yi kira ga isra’ila ta janye killacewar da tayi wa yanki, kuma kotun duniya ta fitar da hukumce dole ne isra’ila ta bude kofofin shigar da kayan agaji zuwa yanki kuma ta tabbata...
    Matakatin shugaban Amurka Donald Trump na nada tsohon fira ministan birtaniya Tony Blair  a matsayin mai ruwa da tsaki cikin alamuran gaza bayan dakatar da bude wuta ya fuskancin turjiya daga kasashen larabawa da kuma na musulmi, Balair shi ne mutum daya da aka ayyana sunansa daga cikin mambobin kwamitin tabbatar da sulhu da trump ya bada shawara na sanya ido bayan kawo karshen yaki tsakanin bangarorin biyu. Akwai damuwa sosai da shakku kan kasancewar Blair daga cikin masu ruwa da tsaki a alamuran yankin, musamman bayan goyon bayan da ya nuna wajen kai wa iraki hari tare da tsohon shugaban Amurka na wancan lokacin a shekara ta 2003 ,a gefe daya kuma yana kare Isra’ila, jamai’an diplomasiyan larabawa sun...
    A yau Asabar al’ummar kasar Ivory Coast ke zaben shugaban kasa wanda ya raba kan kasar inda wasu ke son shugaba Alassane Ouattara ya yi tazarce, wasu kuma na ganin lokaci ne na samar da sabon shugabanci a kasar. Fargaba ta karu sosai tun bayan cire manyan ‘yan takara biyu na jam’iyyun hamayya – wato tsohon shugaban kasar Laurent Gbagbo da Tidjane Thiam, wani kusa a fagen siyasa kuma abokin kawancen Ouattara kafin ya zama abokin hamayya. Rahotanni sun ce Shugaba Ouattara ya yi kira ga magoya bayansa su fito su zabe shi duk da yan kasar da dama na tunanin shi zai lashe zaben,  kafin zaben an samu rikici a sassan kasar da dama inda aka kama daruruwan mutane...
    Rahotanni sun bayyana cewa Tehran za ta karbi bakunci taron ministocin cikin gida na  kungiyar Eco a karon farko a cikin shekaru 15 da nufin karfafa tsaro  da kuma kara fadada yin aiki tare a bangarorin tattalin arzik,i aladu, da kuma harkokin diplomasiya a yankin. Jami’an iran sun tsinkayi irin alfanu da taron kwanaki 2 zai kawo da zai kunshi jerin tattaunawa tsakanin kasashen da sauran bangarori daban –daban. Wannan taron yana zuwa ne lokacin da kasashen dake mambobi a kungiyar suke fuskantar kalubale , da suka hada da rashin tsaro a iyakoki, da aikata muggan laifuffuka da aka tsara, da kuma rashin zaman tabbas a yankin, iran na nufin fadada ajendar ta hanyar yada aladu da amfani da diplomasiya...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15 October 25, 2025 Daga Birnin Sin An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC October 25, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take October 24, 2025
    Ana haka ne Gwamna Babagana Umara Zulum ya kai ziyara ƙaramar hukumar, inda ya gana da Misis Duaka a cibiyar lafiya da misalin ƙarfe 8 na dare, lokacin da sauran ma’aikatan duk sun tashi. Wannan aiki na sadaukarwa, juriya da biyayya ga aikinta, ya sa Gwamna Zulum ya fahimci cewa ta himmatu wajen kula da lafiyar mutanen Mafa, mahaifar sa. Gwamnan dai a wasu ziyarce-ziyarcen da ya kai har sau biyu, ya ware ta, ya kuma yaba wa sadaukarwar da ta yi, tare da yaba mata kan yadda ta tsaya tare da jama’arsa duk kuwa it aba ‘yar asalin yankin ba ne. Kyautar kwazo da rikon amana da ta samu ya zo ne a lokacin da Gwamna Zulum, wanda ya...
    A gun cikakken zaman taro na hudu na kwamitin kolin JKS na 20 da aka gudanar tun daga ranar 20 zuwa 23 ga wannan wata a nan birnin Beijing, an yi bincike da zartas da shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15, inda aka gabatar da jagora da burika kan yadda za a raya kasar a wannan lokaci, kana an tsara taswirar bunkasa kasar Sin a shekaru 5 mazu zuwa. Ga duk duniya, shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar ba shiri na kasar Sin kawai ba ne, kuma ba kasar Sin ba ce wadda ta fara tsara shirin, amma kasar Sin ita kadai ta kiyaye aiwatar da irin shirin. Sirrin tafiyar da harkokin kasar...
    Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa a harkar tsaron sararin samaniya, domin hana ’yan ta’adda na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare. Zulum, ya faɗi haka ne a ranar Juma’a a garin Mafa, bayan wani hari da Boko Haram suka kai. Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam Ya ce, “Babban abin da nake son magana a kai shi ne amfani da jirage marasa matuƙa. An shaida min cewa sun yi amfani da su a Dikwa, kuma hakan abu ne mai tayar da hankali.” Gwamnan ya bayyana cewa yawaitar irin waɗannan jirage a...
    Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke shirin halartar taron shugabannin kungiyar bunkasa tattalin arzikin yankin Asiya da tekun Pacific (APEC) karo na 32 a Koriya ta Kudu da kuma ziyarar aiki a kasar Koriya ta Kudu, an kaddamar da nuna muhimman shirye-shiryen talabijin da fina-finai na rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) a membobin APEC. Za a watsa shirye-shiryen fiye da goma a manyan kafofin watsa labarai 22 a kasashe 14 na yankin Asiya da tekun Pacific, ciki har da Australia, Kanada, Chile, Indonesia, Koriya ta Kudu, Peru, Rasha, Thailand, da Amurka.   Babban darektan CMG Shen Haixiong, ya fada a cikin wani sakon bidiyo cewa, ana fatan wadannan shirye-shiryen talabijin da fina-finai za su...
    “Muna godiya ga sadaukarwar da sojoji da hukumomin tsaro ke yi. Wannan wasa tsakanin tsoffin ’yan wasan Barcelona da tsoffin ’yan wasan Afirka shaida ce ta nasarorin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu wajen dawo da zaman lafiya,” in ji shi. Tsoffin ’yan wasan Barcelona sun isa Nijeriya domin buga wasa da tsoffin ’yan wasan Afirka a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, a ranar Asabar, 25 ga watan Oktoba, 2025. Yayin da Matawalle ke tarbarsu a ofishinsa, ya miƙa saƙon maraba da fatan alheri ga tawagar a madadin Gwamnatin Tarayya da al’ummar Nijeriya, inda ya yi musu fatanalheri. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan...
    Aƙidar Dr Bello abu ne mai saƙin gaske kuma akwai hikima a ciki sosai. Shi ne kuma samar da ingantacciyar kiwon lafiya wand aba wai sai kana da kuɗi mai yawa ba. Tsarinsa shi ne haɗa yi wa mutane aiki, ilimantar da su tared fda kuma tsugunar da su. Wannan mataki ne da yake tabbatar da an samun cikin gaggawa da kuma sauƙin gaske.. Daga Legas zuwa Kano, daga Ondo zuwa Kuros Riba, kungiyar CFDF tana tafiya da kayan aiki na tafi da gidanka da kuma rundunar likitoci masu tiyata na sa kai, masu aikin jinya, da ma’aikatan jinya. Kowace manufa asibiti ce mai motsi – duba marasa lafiya, yin hadaddun tiyata, da bayar da shawarwari da tallafin abinci mai...
    Rundunar Sojin Najeriya za ta fuskanci babban sauyi wanda zai tilasta wa manyan sojoji yin ritaya daga aikinsu. Rahotanni sun bayyana cewar akalla Janar-Janar 60 ne ake sa ran za su yi ritaya sakamakon sabbin sauye-sauye da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Hafsoshin Tsaro. ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Sanarwar da aka fitar a ranar Juma’a ta tabbatar da sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaro tare da wasu hafsoshi. Janar Laftanar Olufemi Oluyede, wanda a baya shi ne Babban Hafsan Sojin Kasa, shi ne yanzu sabon Babban Hafsan Tsaro. Janar Meja Waidi Shaibu shi ne...
    “Gudanar da harkokin kuɗaɗe ba bayar da taimako ba ne, haƙƙi ne.”  Ƙoƙarin Cike Gibi Tare Da Gina Makoma Mai Kyau Lokacin da OPay ya shiga fannin harkokin kuɗaɗe na zamani a Nijeriya, ƙalubalen ya kasance bayyane suke, kusan rabin yawan mutanen Nijeriya ba su da damar samun shiga harkokin kuɗaɗe. Waɗanda suka kafa kamfanin sun gano cewa yawancin ‘yan Nijeriya sun yin isa da bankuna, tsarin yana haifar da jinkiri, kuma tsarin yana da barazana mai yawa. OPay ta kasance mai sauƙin gudanarwa, wani tsarin kuɗi na wayar hannu da ya dace da rayuwar yau da kullum ba tare da tangarda ba. Daga biyan kuɗi ta walat zuwa biyan kuɗin kayayyakin more rayuwa, daga sayan katin waya zuwa mu’amaloli...
    Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, wanda Kwamishinan Ruwa, Alhaji Aminu Dodo Iya, ya wakilta, ya jaddada cewa sarautun gargajiya su ne ginshiƙin zaman lafiya da ci-gaban al’umma. Ya ce shugabannin gargajiya na taka rawa wajen haɗa kan jama’a da gwamnati, tare da tabbatar da ɗorewar cigaba a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales October 25, 2025 Manyan Labarai Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce October 25, 2025 Labarai Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa October 25, 2025
    Ya ƙara da cewa cibiyar Centre for Energy Research and Training (CERT) ta  jami’ar ABU, wadda aka kafa tun 1976, tana aiki tare da IAEA da kuma ƙasashe kamar Amurka, da Rasha da China, kuma ba ta taɓa gudanar da wani shiri na makamin nukiliya ba. A cewarsa, “ABU tana ci gaba da sadaukar da kai wajen inganta kimiyya da fasaha don ci gaban ƙasa da kuma tabbatar da zaman lafiya ta hanyar amfani da makamashin nukiliya ta hanya mai amfani da jama’a.” ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu October 25, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi October 25, 2025 ...
    Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo Wannan inganci ba wai alama kawai ba ce. Tun daga shekarar 2023, hukumar ta sauƙaƙa sama da Naira biliyan 10 na mayar da kuɗin masu amfani don sulhu kai tsaye, mai iya bin sawu wanda ke nuna cewa dawainiya da gaskiya za a iya auna ta da kuɗi, ba wai da alkawari kawai ba. Jarumta a Zamanin Intanet Wataƙila mafi girman ƙarfin gwiwar FCCPC ya bayyana ne a shekarar 2025 lokacin da ta ɗora tarar Dalar Amurka miliyan 22 kan Meta Platforms saboda ayyukan amfani da bayanai ta...
    Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Bai kamata a yi mummunan amfani da kwamitin tsaron ba ko kuma a yi amfani da shi don dalilai na siyasa Jakadan Iran kuma wakilin dindindin a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani, ya bayyana cewa: An gwada Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya sosai ta hanyar ayyukan ta’addanci da kuma amfani da dabarunta na siyasa. Ya ce: “Dole ne kwamitin tsaro ya cika nauyin da ke kansa da mutunci, inganci, kuma ba tare da son kai ba. Babu wani memba, komai karfi da zai iya amfani da wannan cibiyar ba bisa ka’ida ba ko kuma ya yi amfani da shi don dalilai na siyasa ko na bangare guda.” A jawabinsa a Majalisar...
    Tsohon shugaban hukumar leƙen asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Yaƙin da aka ɗora wa Iran ya canza daidaiton da ke tsakanin Sahayonayya da Amurka Tsohon shugaban hukumar leƙen asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), Hussein Ta’ib, ya ce: Yaƙin kwanaki 12 da gwamnatin sahayoniyya ta ɗora wa Iran, ba wai kawai bai cimma komai ga Isra’ila ba ne, har ma ya canza daidaiton dabarun Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila gaba ɗaya. A lokacin taron tattaunawa na 31 na ƙungiyar Jaruman Musulunci a Qom, Hussein Ta’ib ya ce: “Dakarun kare juyin juya halin Musulunci da sojojin Iran sun kalubalanci masu girman kai inda suka kai wani mataki cikin saurin na zarce lissafin...
    Mataimakin babban kwamandan rundunar sojin Iran kan hadin gwiwa ya jaddada cewa: Sojojin Iran a shirye suke su fuskanci kowace barazana Mataimakin Babban Kwamandan Rundunar Sojin Iran kan Hadin Gwiwa, Rear Admiral Habibullah Sayyari, ya ce: An zabi Sojojin Iran daga cikin mafi kyawun matasa a kasar kuma suna shirye su fuskanci kowace barazana. A gefen bikin bude gasar cin kofin duniya ta 4 ta sojojin masu harba kibau (SIZM 2025), wadda rundunar sojin sama ta shirya a kungiyar masu harbi a ranar Juma’a da yamma, Rear Admiral Sayyari ya yi magana da manema labarai game da matakin shirye-shiryen Sojojin da kuma rawar da wasanni ke takawa wajen inganta karfinsu. Ya jaddada cewa, “Wasanni suna da matukar muhimmanci ga lafiyar...
    Shugaban kasar Venezuela yayi tsokaci kan matakin sojin Amurka yana mai cewa Amurka tana son ƙirƙiro yaƙi a yankin Shugaban kasar Venezuela Nicolás Maduro ya zargi Amurka da yunkurin tayar da sabon yaki a kan kasarsa, bayan rahotannin da ke cewa; Amurka na gudanar da shirin soja na kai hari kan wuraren samar da hodar iblis a Venezuela. Maduro ya ce a cikin wani jawabi da ya gabatar ta gidan talabijin: “Suna kirkirar yaki ne domin tabbatar da ta’addancin da suke yi wa Venezuela… Suna son mayar da batun miyagun kwayoyi ya zama hujjar sabon mamayar sojoji a Latin Amurka.” Ya kara da cewa gwamnatinsa “ba za ta bari wani karfi na kasashen waje ya keta ikon Venezuela ba,” yana...
    Bangarorin Falasdinawa sun amince a birnin Alkahira kan yadda za a tafiyar da Gaza a nan gaba Bangarorin Falasdinawa da suka yi taro a birnin Alkahira a ranar Juma’a sun sanar da amincewarsu kan wasu muhimman batutuwa da suka shafi gudanar da yankin Gaza da kuma ci gaba da tabbatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, da kuma abu mafi muhimmanci na kafa kwamitin da za a mika masa ikon wucin gadi na tafitar da al’amuran Falasdinawa a Gaza. Wata sanarwa da bangarorin suka fitar a karshen tarukansu a babban birnin Masar ta bayyana cewa, bisa gayyatar Jamhuriyar Larabawa ta Masar, karkashin jagorancin Shugaba Abdul Fattah el-Sisi, da kuma ci gaba da kokarin ‘yan uwa masu shiga tsakani a Masar, Qatar, da...
    Sauyin shugabannin tsaro dai ya nuna matakin da Tinubu ke ɗauka wajen sake fasalin tsaro, amma kuma ya buɗe sabon babi na tattaunawa kan yadda ake kula da tsofaffin hafsoshin da suka ba ƙasa hidima tsawon shekaru. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi October 25, 2025 Manyan Labarai Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin October 25, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe October 25, 2025
    Mazauna unguwar Tudun Wada da ke garin Shendam a Jihar Filato sun zargi wasu jami’an ’yan sanda da ba wa ’yan daba kariya wajen rusa gidajensu. Shaidu sun ce sama da ’yan sanda 100 ɗauke da makamai ne suka isa yankin da misalin karfe 5 na safiyar Laraba, suka ba wa wasu ’yan daba kariya yayin da suke lalata gine-ginen jama’a Lamarin ya jawo zanga-zangar da mazauna yankin, ciki har da mata da yara, suka gudanar don nuna adawa da abin da suka kira “cin zarafi daga jami’an tsaro.” Mazaunan sun bayyana cewa rushewar gidajen ta faru ne da haɗin gwiwar iyalan Fuanter duk da cewa ana shari’a a gaban kotun ɗaukaka ƙara kan mallakar filayen. Sun ce suna da...
    Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin, ya bayyana cewa su na nazarin dokoki guda 69 da kuma buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙudirin ƙirƙirar ƙananan hukumomi 278 bisa ga tsarin kundin mulkin 1999. Barau, wanda shi ne shugaban Kwamitin Bita na Tsarin Mulki a majalisar dattawa, ya bayyana hakan ne a taron haɗin gwuiwa da kwamitocin majalisar dattawa da kwamitocin majalisar wakilai kan gyare-gyaren dokokin tsarin mulki da suka gudanar a Lagos. Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta Ya jaddada cewa an dauki lokaci mai tsawo wajen tattaunawa da al’umma da masu ruwa-da-tsaki da ƙungiyoyi daban-daban, domin kawo waɗannan ƙuduri...
    Najeriya na fama da ɗaya daga cikin mafi munin matsalar jinƙai ta yunwa, talauci, da rashin abinci mai gina jiki. Rahoton Yanayin Ci-Gaban Nijeriya da Bankin Duniya ya fitar a watan Oktoba, ya nuna mutane miliyan 139 a ƙasar na rayuwa cikin talauci a shekarar 2025. Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da rahoton, da cewa sauye-sauyen da ta yi a fannin tattalin arziki na haifar da sakamako mai kyau. Aminiya ta gudanar da bincike don gano gaskiyar halin da ’yan Nijeriya ke ciki a birane da ƙauyuka. Wakilinmu ya samu damar shiga cibiyoyin kula da masu fama da rashin abinci mai gina jiki da Ƙungiyar Likitoci ta Duniya (MSF) ke tallafawa a Kano da Maiduguri, inda ya gano mummunan tasirin...
    Rashin Biyan Yan-fansho Bisa Lokaci Ta tabbata a lokacin mulkin Kwankwaso, “yan fansho a Kano, kan jira tsawon Watanni zuwa Shekaru ba tare da an biya su hakkokinsu na barin aiki ba. Haka ɗan-jummai Ganduje, yakan dan fara biyan hakkokin “yan fanshon, sai kuma a ga ya watsar. Sai a dauki tsawon lokaci yana ɓaɓatun za a ci gaba da biya, amma sai a ji shiru. Sai aka wayi gari karɓar fansho, musamman giratuti, ya zama tamkar tafiya Lahira, yau ne? Gobe ne? Babu wata cikakkiyar amsa!. Haƙiƙa kwata-kwata babu tausai, mutane sun kwashe akasarin Shekarunsu na haihuwa suna masu hidimtawa ƙasa dare da rana, cikin yanayi na sanyi, ruwan sama da garjin rana, dole ne su fito, su aje...
    Mahalifinsa, Chief Thomas Osen Ekpemupolo, da mahaifiyarsa, Mrs. Ewe Ekpemupolo, sun rayu cikin al’umma mai arziƙin mai a lokacin da ake tsaka da nema a yi wa yankinsu adalci. Daga cikin wannan rikicewar ya taso mutum wanda daga baya zai zama ɗan gwagwarmayar Niger Delta don neman daraja, adalci, da samun ikon gashin kai. Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta A tsakiyar shekarun 1990, arzikin mai na Nijeriya yana samu wadata a wasu wurare amma ya zama ana barin al’ummomi masu arziƙin mai cikin talauci, gurɓawa, da kuma rashin muryar magana. Ga matashin Tompolo, yin shiru wannan bai zama zaɓi ba.   Gwagwarmaya Da...
    Shugaban gwamnatin kasar Lebanon Nawwaf Salam ya bayyana cewa: Tun da ya kafa gwamnati yake aiki da dukkanin hanyoyi domin yin matsin lamba akan HKI ta daina keta hurumin kasar, sannan kuma ta janye daga wuraren da ta shiga, tare da sakin fursunonin da take rike da su.” Nawwaf Salami ya kara da cewa; Bude kafar diplomasiyya da aiki da ita a wannan fage, bai bayar da wani sakamako ba, watakila kuma zai dauki lokaci mai tsawo a nan gaba.” Shugaban gwamnatin kasar ta Lebanon ya kuma ce; A yanzu muna cikin halin yaki ne da “Isra’ila”, wani lokaci ya yi tsanani, wani lokacin kuma ya yi sauki,illa iyaka muna kokarin ganin an kawo karshen hakan.” Dangane da batun bude...
    Shugaba Gustavo Petro ya ce, ba wai kawai ba ya wata mu’amala ta kasuwanci da Amurka ba ne, ba shi ma da koda dala kwaya daya a cikin wani asusu na bankunan Amurkan balle a ce an rufe shi. Gustavo ya kara da cewa; ko kadan ba zai taba rusunawa a gaban Amurka ba, ba kuma zai ja da baya ba. A jiya Juma’a da marece ne dai Baitulmalin Amurka ya sanar da kakaba wa shugaban kasar ta Columbia takunkumi. Gustavo ya kuma ci gaba da cewa; Yadda yake fada da yaduwar muggan kwayoyi na shekaru masu tsawo, shi ne ya sa Amurkan ta dauki wannan irin matakin akansa alhali kasarsa Columbia tana taimakawa wajen hana Amurkawan shan hodar Iblis....
    Kungiyar kwallon kafa ta “Futsal” ta matan Iran ta zura kwallaye 14-0 a wasan da ya hada ta da takwararta ta kasar Bahrain mai masaukin baki. A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai aka bude wasannin nahiyar Asiya na kwallon kafar Futsal a kasar Bahrain. A wasan farkon, kungiyar ta Iran ta sami nasara akan takwararta ta Hong kong ta hanyar zura kwallaye shida. Wasa na biyu da Iran din ta yi shi ne da kungiyar kasar Bahrain, da ta sami galaba da kwallaye 14 da 0. ‘Yan wasan na Iran sun kunshi Fatima Shukrani, Niyayash Rahmani, Dhanaz Bakiri, Haidis Yari da kuma Narjis Amir Muhsini. Ya zuwa yanzu dai kungiyar kwallon Futsal ta Iran tana da maki...
    Babban magatakardar MDD Antonio Gutrress ya bayyana cewa majalisar tana da bukatuwa da a yi kwaskwarima da gyare-gyare. Gutrress dai ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabin cika shekaru 80 da kafuwar MDD. Gutrress ya kuma ce, tare da cewa ayyukan da Majalisar take aiwatarsa suna da matukar muhimmanci,amma kuma halarcinta yana tangal-tangal, sannan kuma ya kara da cewa an dade ana sauraron a yi ma ta kwaskwarima.  A wani sashe na jawabin nashi, ya zargi wasu daga cikin mambobin MDD da cewa a lokuta da dama suna yin abubuwan da suke cin karo da dokokin majalisar, da hakan yake sa ake yin shakku akan ita kanta majalisar ta dinkin duniya. Har ila yau, Guterres ya ce; Majalisar...
    Ma’aikatar kiwon lafiyar kasar Lebanon ta sanar da shahadar mutum daya da kuma jikkatar wani sanadiyyar harin da HKI ta kai wa wata mota a garin Zudhar dake gundumar Nabadhiyya. Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta bayar da laabrin cewa a jiya  Juma’a sojojin HKI sun bude wuta a cikin Lebanon daga kan iyakar ‘alhamamis”. Bude wutar da manyan bindigogi ya kuma shafi kudancin birnin al-khayam. Har ila yau birnin na alkhayam ya fuskanci wasu hare-hare daga HKI da ta yi amfani da jiragen sama marasa matuki. HKI tana ci gaba da keta tsagaita wutar yaki da aka yi tun a 27 ga watan Aprilu 2024. Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies...
    Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Gombe, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), ya rasu a hatsarin mota. Gwamnatin Jihar Gombe ce, ta sanar da rasuwar cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Watsa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Juma’a. Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri Sanarwar ta ruwaito cewa Bello ya rasu a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe, bayan aukuwar wani mummunan hatsarin mota. “Gwamnatin Jihar Gombe na cikin jimamin sanar da rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), sakamakon a hatsarin mota da ya rutsa da shi a kan hanyar Malam Sidi...
      Guo ya kara da cewa, “Abubuwan da gwamnatin Amurka take aikatawa suna da yiwuwar haifar da rashin fahimta da dora laifi ga wanda bai ji ba bai gani ba, kuma kwata-kwata ba su dace ba. Kasar Sin tana kira ga Amurka ta dakatar da kai hare-haren shafin intanet kan muhimman kayayyakin more rayuwa na kasarta nan take. Bugu da kari, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka wajaba don kare ‘yancin kanta na shafin intanet da kuma tsaronta yadda ya kamata.” (Abdulrazaq Yahuza Jere) ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan October 24, 2025 Daga Birnin Sin...
    Shirin Inganta Noma da Kula da Sauyin Yanayi na Soil Values, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Dillalan Kayayyakin Aikin Gona ta Kasa (NAIDA) ta Arewa maso Yamma, ya ƙaddamar da sabon tsari domin sauƙaƙa samun kayayyakin gona ga ƙananan manoma a yankunan Arewacin Najeriya, da ake kira “one-stop shop a turance. Jami’ar shirin ta kasa Misis Medina Ayuba Fagbemi, ta bayyana cewa za a samar da shagunan tafi-da-gidanka guda tara da za su kai kayayyaki zuwa sama da al’ummomi 20 a jihohin Kano, Jigawa da Bauchi, inda ake sa ran shirin zai amfanar da kusan ƙananan manoma 7,000. Ta ce tsarin zai taimaka wajen kusantar da ingantattun iri, taki da magungunan kashe kwari ga manoma, tare da samar da...
    Ya bayyana cewa sarakuna suna taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba, musamman a fannin ilimi, inda ya ce zai tabbatar yara sun koma makaranta. Haka kuma, ya ce zai goyi bayan gwamnati a ɓangaren kiwon lafiya da tsaro, domin inganta rayuwar jama’a. Sabon Sarkin, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kula da ilimi a matakin farko (SUBEB) ta Jihar Bauchi, ya bayyana farin cikinsa da godiyarsa ga Allah da Gwamna Bala Muhammad saboda wannan dama da ya samu. Ya yi alƙawarin yin aiki tuƙuru domin ci gaban masarautarsa da Jihar Bauchi gaba ɗaya, tare da kira ga jama’ar Duguri da su haɗa kai wajen gina masarautar. “Mu mutanen Duguri a shirye muke mu taimaka wa gwamnati a duk abin...
    Ya ce Hukumar Binciken Ƙasa ta Nijeriya (NGSA) za ta jagoranci kwamitin, domin ita ce ke da ikon tattara bayanan ma’adinai na ƙasa baki ɗaya.  “NGSA ta yaba da ƙoƙarin gwamnatin Jihar Kaduna bisa gaskiya da bayyana bayanai, tare da yin kira da a gudanar da binciken tabbatarwa mai zaman kansa,” in ji shi. Ya ƙara da cewa wannan haɗin gwiwar zai ƙara goyon bayan masu zuba jari a sashen ma’adinai na Nijeriya, tare da faɗaɗa bayanan kimiyyar ƙasa, wanda zai taimaka wajen haɓɓaka tattalin arzikin ƙasa ta hanyar albarkatun ma’adananta. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri October 24, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya October...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa October 24, 2025 Daga Birnin Sin An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan October 24, 2025 Daga Birnin Sin Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15  October 24, 2025
    Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar. An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda. Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a...
    Jam’iyyar ADC ta nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana wa ’yan Najeriya ainihin dalilin da ya sa ya sauya hafsoshin tsaron ƙasa ba zato ba tsammani. Aminiya ta ruwaito yadda shugaban ƙasa ya sauya hafsoshin tsaron da ya naɗa shekaru biyu da suka wuce. Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri ’Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan Neja A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce jam’iyyar ta damu ganin yadda aka yi sauyin ba zato ba tsammani bayan jita-jitar yunƙurin juyin mulki. “Ko da yake shugaban ƙasa yana da ikon yin irin waɗannan sauye-sauye, amma mum damu da wannan mataki biyo bayan...
    Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa wannan zaman sulhu da ɓarayin daji da ake yi al’umma ce take yi ba wai gwamnati ba, ita gwamnati tana iya yin sulhu da ɗan bindigar da ya tuba ya yarda da zaman lafiya kuma ya ajiye mukaminsa. A cewarsa, rawar da gwamnati take iya takawa shi ne, ta ƙarfafa zaman lafiya, sannan ta tabbatar an bi doka da oda a cikin al’umma. Ya ce abubuwa da gwamnati ke lura da su shi ne, al’umma ta mori zaman lafiya domin bunƙasar tattalin arziki da sauran su.  Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya rage ƙarfin harkokin rashin tsaro a Jihar Katsina....
    Bugu da kari, Han ya ce, zamanantar da aikin gona da raya yankunan karkara tana da matukar muhimmanci a cikin aikin zamanantarwa irin ta kasar Sin, saboda haka ya kamata a ba wannan bangare fifiko. Ya ce shawarwarin da kwamitin kolin JKS ya gabatar na jaddada bukatar mai da raya harkoki masu alaka da aikin gona da raya yankin karkara da kyautata rayuwar manoma, a matsayin abu mai matukar muhimmanci, da tabbatar da bunkasar birane da yankin karkara na bai daya, da kuma hanzarta wajen inganta karfin kasar a fannin raya aikin gona.   A yayin taron, direktan hukumar raya kasa da gyare-gyare ta kasar Sin, Mr. Zheng Shanjie ya bayyana cewa, “kirkira da habaka sabbin abubuwa” na nufin habakawa...
    Ofishin kula da ayyukan binciken sararin samaniya na ’yan sama jannati, ya ce za a harba kumbon Shenzhou-21 a lokaci mai dacewa a kwanan nan. Yana mai cewa an riga an kai kumbo da rokar da za ta harba kumbon, zuwa wurin harbawa a yau Jumma’a. A cewar ofishin, an kai kumbon Shenzhou-21 da zai dauki ’yan sama jannati da kuma rokar Long March 2F Yao-21 mai dauke da kumbon zuwa wurin harbawa a yau Jumma’a. A halin yanzu, kayayyakin aiki a wurin harba kumbon suna cikin kyakkyawan yanayi. Kana za a gudanar da bincike daban daban da kuma gwaje-gwajen hadin gwiwa kamar yadda aka tsara kafin harbawa. Bisa shirin da aka tsara, za a harba kumbon a wani lokaci...
    Kasar Iran ta yi Allah wadai da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan kasar Lebanon Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta yi Allah wadai da hare-haren da yahudawan sahayoniyya suka kai ta sama kan yankunan kudancin Lebanon da kwarin Beka’a na kasar. Baqa’i ya bayyana hare-haren da ‘yan sahayoniyya suka kai a ranar Alhamis a yankunan kudancin da kwarin Beka’a na Lebanon, wadanda suka yi sanadiyyar shahada da kuma raunata wasu fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da dalibai a wata makaranta a kwarin Beka’a, tare da bayyana harin a matsayin “laifi na ta’addanci” kuma ya yi suka mai tsanani kan su. Baqa’i ya gabatar da alhini da...
    Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha ya bayyana cewa: Kasashen Yamma sun taka dokokin kasa da kasa a batun Iran Mataimakin Ministan Harkokin Wajen kasar Rasha Sergei Ryabkov ya soki matakan ƙasashen Yamma, ciki har da harin soji da suka kai wa Iran da kuma ƙoƙarinsu na sake Sanya mata takunkumi, yana mai cewa, “A wannan yanayin, ƙasashen Yamma sun taka dokokin ƙasa da ƙasa.” Jaridar Kommersant ta ruwaito cewa: Ryabkov ya yi waɗannan kalaman ne a lokacin wani shirin yanar gizo mai taken “Tarihi da Siyasar Yanzu na Manufofin Nukiliya na Rasha da Diflomasiyyar Jama’a a Bangaren Nukiliya,” wanda Cibiyar Makamashi da Tsaro ta shirya. Yayi nuni da cewa: “Yanayin Iran, ƙasashen Yamma sun taka dokokin ƙasa da ƙasa...
    Shugaban kasar Amurka Trump ya ce: Za su dauki matakin soji kan kasar Venezuela nan ba da jimawa ba Shugaban Amurka Donald Trump ya yi nuni da cewa kasarsa za ta iya fara yaki da “masu safarar miyagun kwayoyi nan ba da jimawa ba,” yana mai cewa, “Za su dauki mataki ta hanyar kutsawa ta kasa a kasar Venezuela,” yana mai nuni da yiwuwar shiga tsakani na soja ko ayyukan leken asiri. A martanin da ya mayar, Shugaba Trump daga baya ya musanta rahotannin cewa: Jiragen yakin Amurka sun yi shawagi a kusa da kan iyakar Venezuela, yana mai jaddada cewa: “Ba gaskiya ba ne cewa: Amurka ta aika da jiragen yakin sama kusa da Venezuela.” Trump ya shaida wa...
    Gwamnatin kasar Iraki ta yi Allah wadai da matakin da Majalisar Dokokin Isra’ila “Knesset” ta dauka na mamaye yankin Yammacin Kogin Jordan da kuma gine-gine matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida ba bisa ka’ida ba Ma’aikatar Harkokin Wajen kasar Iraki ta bayyana Allah wadai da amincewa da kudurorin biyu na Majalisar Dokokin Isra’ila “Knesset” ta yi da su da nufin sanya kwace iko da mallakar yankin Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye da kuma gudanar da matsugunan yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida ba bisa ka’ida ba. Ma’aikatar ta ce a cikin wata sanarwa cewa: “Tana bayyana kakkausar suka da Iraki ta yi kan amincewar da Majalisar Dokokin Isra’ila ta yi da kudurorin biyu da nufin kwace iko da mallake yankin Yammacin...
    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, wanda kuma shi ne sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS), ya jagoranci wani taron karawa juna sani a ranar 27 ga watan Augusta, domin jin ra’ayoyin wadanda ba ‘yan jam’iyyar ba, dangane da shawarwarin da kwamitin kolin JKS ya gabatar game da tsara shirin raya kasa na shekaru 5 karo na 15, da ke da nufin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar. (Fa’iza Muhammad Mustapha) ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu October 24, 2025 Daga Birnin Sin Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da...
    Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya naɗa babban ɗan uwansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sabon Sarkin Masarautar Duguri. Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Aminu Hammayo ne, ya bai wa sabon Sarkin takardar naɗin a madadin gwamnan, a wani biki da aka gudanar a fadar sarkin Duguri, da ke Ƙaramar Hukumar Alkaleri, a ranar Juma’a. Ƙungiya ta tallafa wa ɗaliban makarantar masu buƙata ta musamman a Gombe ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa A yayin bikin, Sakataren Gwamnatin Jihar, ya shawarci sabon Sarkin da ya ci gaba da mara wa manufofi da shirye-shiryen gwamnati baya, domin samar da ci gaba mai ɗorewa a jihar. A nasa jawabin, sabon Sarkin Duguri, Alhaji Adamu Mohammed, ya...
    Hammayo ya shawarce shi da ya gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci tare da haɗa kan ƙabilu don tabbatar da zaman lafiya. A baya-bayan nan ne Gwamna Bala Mohammed ya rattaba hannu kan dokar kafa sabbin masarautu 13 a jihar. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya October 24, 2025 Manyan Labarai Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa October 24, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu October 24, 2025
    Ƙungiyar Arewa Unity Women in Media, ta kai tallafi Makarantar Masu Buƙata ta Musamman da ke Gombe, domin taimaka wa gwamnati wajen kula da rayuwar ɗaliban da ke da buƙata ta musamman. Tallafin ya ƙunshi gidajen sauro, bargo da tabarmi, wanda aka raba wa ɗaliban a lokacin bikin miƙa kayan tallafin. ’Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan Neja ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa Shugabar ƙungiyar, Lois Hassan daga GMTV Gombe, tallafin na da nuna kulawa da ƙauna ga ɗaliban, tare da tabbatar musu cewa al’umma ba ta manta da su ba. Ta ƙara da cewa ƙungiyar Arewa Unity Women in Media ƙungiya ce mai zaman kanta da ke gudanar da...
    Rundunar ’yan sanda ta kama wani matashi ɗan shekara 29, mai suna Abubakar Isah Mokwa ɗalibi da yake karatun digiri na biyu a tsangayar Tattalin Arziki na Noma a Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai, Jihar Neja. An kama ɗalibin ne bisa zarginsa da sukar Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago. Rahotanni sun ce an an kama Abubakar Mokwa ne a wajen harabar jami’ar da yake da masauki a Lapai a ranar Alhamis bayan wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya caccaki gwamnan kan rashin aikin yi. ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu...
    Tawagar kamfanin na Rano Air a wurin ganawa da gwamnan, ta haɗa da Babban Manajan (Ayyuka), Abah O. Godwin; da Accountable Manager Alhaji Lawal Sabo Bakinzuwo; da Shugaban Sashin Ayyuka na ƙasa Bashir Abdullahi Wudilawa; da Shugaban Sashin Bunƙasa Harkokin Kasuwanci na kamfanin, Auwal Sulaiman Ubale. Jami’an kamfanin sun tabbatarwa gwamnan cewa kamfanin na Rano Air zai samar da nagartacciyar hidima abar dogaro, mai inganci kuma mai haba-haba ga kwastomomi, ta yadda za a samu sauƙin tafiye-tafiyen kasuwanci da bunƙasa harkokin tattalin arziki a faɗin jihar da Arewa Maso Gabas baki ɗaya. “Gwamna Inuwa Yahaya ya yi maraba da wannan ci gaba, inda ya bayyana hakan a matsayin wata shaida kan yadda Jihar Gombe ke da zaman lafiya da kwanciyar...
    Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Juma’a cewa, shugaban kasar Xi Jinping zai halarci taron shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin ta kasashen Asia da Pasifik (APEC), karo na 32 a Gyeongju na Korea ta Kudu, bisa gayyatar shugaban kasar Lee Jae-myung. Taron zai gudana ne daga ranar 30 ga watan Oktoba zuwa 1 ga watan Nuwamba, kana shugaba Xi Jinping zai yi ziyarar aiki a kasar. (Fa’iza Muhammad Mustapha) ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta October 23, 2025 Daga Birnin Sin Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa October 23, 2025 Daga...
    Shugaba Tinubu, ya gode wa tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, da sauran tsoffin hafsoshin bisa gudunmawar da suka bayar. Ya kuma bukaci sabbin hafsoshin da su tabbatar sun cancanci nadin da aka musu ta hanyar nuna ƙwarewa, haɗin kai wajen tsaron Nijeriya. “Shugaban ƙasa ya bukaci sabbin hafsoshin tsaro da su tabbatar da cewa sun cancanci nadin da aka musu ta hanyar nuna ƙwarewa, faɗakarwa, da zumunci wajen tsaron ƙasa,” in ji sanarwar. Sanarwar ta bayyana cewa dukkanin sabbin naɗin za su fara aiki nan take. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi October 24, 2025 Labarai Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule October 24, 2025...
    ’Yan Sanda sun sake kama dan gwagwarmaya kuma mamallakin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, bayan wata kotun Majistare da ke Abuja, ta bayar da belinsa.  An sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa tare da wasu mutum 12 a ranar Juma’a. Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike Alƙalin kotun, Abubakar Sai’id ne, ya bayar da belin Sowore da wasu mutum 12 da aka tuhuma da tayar da hankalin jama’a, sakamakon zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin. Lauyan Sowore, Tope Temokun, ya zargi ’yan sanda da yin amfani da karfi, inda suka yi awin gaba ba tare da wani bayani ba....
    Mahaifin Rukayya, Muhammad Adamu mazaunin ƙauyen Bayan Dutse da ke Wailo, a gundumar Kubi cikin ƙaramar hukumar Ganjuwa a ranar 17 ga watan Oktoba ya kai rahoton caji ofis ɗin Soro ya ke shaida cewar wani matashi mai suna Auwal Dahiru mai shekara 17, ya kai farmaƙi wa yarsa da ƙoƙarin kasheta da kwaƙule mata idanuwanta.  Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil a ranar Litinin, ya ce, lokacin da ‘yansanda suka samu rahoton faruwar lamarin cikin gaggawa a ƙarƙashin Baturen ɗansanda da ke kula da caji ofis ɗin Soro, CSP Aliyu Mohammad Goni, sun kai agaji inda lamarin ya faru. A lokacin da aka ɗauki Rukayya zuwa asibitin koyarwa na...
    Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaron Kasa. Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sunday Dare, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, ya fitar a ranar Jumma’a. An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike A cewar sanarwar, an nada Janar Olufemi Oluyede, wanda shi ne Shugaban Sojin Ƙasa, a matsayin Sabon Babban Hafsan Tsaron Ƙasa. An kuma naɗa Manjo Janar W. Shaibu a matsayin Shugaban Sojin Ƙasa, Air Vice Marshal S.K. Aneke a matsayin Shugaban Rundunar Sojin Sama, da Rear Admiral I. Abbas a matsayin...
    Ministan Babban Birnin Tarayya , Nyesom Wike, ya yi gargadin cewa irin yadda gwamnonin jam’iyyar PDP ke tafiyar da al’amuranta a yanzu, zai iya sanadin rushewar jam’iyyar. Wike, ya bayyana haka ne a lokacin da yake hira da ’yan jarida a Abuja ranar Juma’a, inda ya zargi gwamnonin PDP da gaza magance rikicin jam’iyyar yadda ya kamata. An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027 Rahotanni sun nuna cewa akwai rashin jituwa tsakanin Wike da gwamnonin PDP. Jam’iyyar na shirin gudanar da babban taronta na kasa a watan Nuwamba a birnin Ibadanna  Jihar Oyo, amma wasu rahotanni na cewar magoya bayan Wike...
    A shekara biyu kaɗai,ya yi ƙoƙarin maida Jihar Kaduna da aka sani da rarrabuwar kai, yanzu ta koma tsintsiya ɗaya sanadiyar hakan. Yin gyara ta hanyar ci gaba Gwamna Sani ya hau kan karagar mulki ne a shekarar 2023 ba a matsayin wanda ya iya lamarin siyasa sosai ba, sai dai mai son kawo agyara. Aikinsa na farko ba siyasar bace —mutane ne yafi maida hankali kansu. Ya fara ƙaddamar da lamarin gaggarumin ci gaban ƙauyuka ta yadda abin ya zama a kowace ƙaramar hukumar akwai aikin da ake yi.Gina hanyoyi, asibitoci,  makarantu, kasuwanni an fara gigginasu a ƙananan hukumomi  23 . Cikin ci gaban daya samu sun haɗa da: Haɓaka ƙananan asibitoci 225 inda aka mayar da su matsayi...
    Kafin ya zama gwamna, ya kasance Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Delta, inda ya yi ƙaurin suna wajen yin adalci, kwanciyar hankali da kuma zurfin fahimtar shugabanci. Wannan gogewa ta aikin doka, ta zama ginshiƙin nasararsa na gudanarwa. Kazalika,ya ba shi damar daidaita hangen nesa da tuntuɓa tare da yin taka- tsan-tsan wajen aiwatar da ayyukansa. Ajandarsa Ta “MORE Agenda” Ajandarsa ta ayyukan da yake ƙuzun aiwatarwa, ƙarƙashin “MORE Agenda”, Gwamna Oboreɓwori, ba wai kawai taken ba ne; tsari ne na aiki wanda ya ƙunshi kowane ɓangare na ayyukan da son aiwatarwa ƙarƙashin mulkinsa A Ƙarƙashin Jagorancinsa: An kammala ayyukan tituna sama da 513 da suka shafe kusan kilomita 1,500, ban da kuma waɗanda ake kan ci gaba da gudanarwa a...
    Rundunar ’Yan Sandan jihar Yobe ta ce ta cafke wani shugaban mazaba na jam’iyyar APC a karamar hukumar Karasuwa bisa zarginsa da hannu a kisan wata mata. Rundunar ta ce ta samu nasarar ce a binciken da take yi kan wata gawar da aka gano a kusa da Jami’ar Tarayya da ke Gashuwa a makon da ya gabata. Gwamnan Neja ya ba dukkan iyalan wadanda suka kone a gobarar tankar mai N1m Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027 A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ’yan sanda daga sashin karamar hukumar Bade sun kama wani mutum mai suna Abdulmumini Garba, mai shekaru 60, dangane da mutuwar matar...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu October 24, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji October 24, 2025 Manyan Labarai Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa October 24, 2025
    Wasu jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) guda uku da ke hanyarsu ta zuwa jihar Anambra domin shirye-shiryen zaben gwamna na ranar 8 ga Nuwamba, sun shiga hannun ‘yan bindiga a jihar Kogi. Rahotanni daga mazauna yankin sun bayyana cewa an yi garkuwa da jami’an ne a ranar Talata, a ƙauyen Aloma da ke ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi. Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC Sienna da suka ke tafiya da ita ya bayyana a cikin wani kiran waya cewa ƴan bindigar sun tare hanya, suka buɗe musu wuta, har suka lalata gilashin gaban motar, lamarin da ya tilasta...
    Ga Dukkan Alamu Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti Waɗannan ginshiƙai, an tsara su ne bisa manufofin sanya hannun jari a cikin dukkanin ƙananan hukumomi 16 na jihar. A cikin shekaru uku, manyan ayyuka 577 zuwa 368 aka kammala, sannan kuma 209 da ake kan gudanar da su a halin yanzu, sun shafi garuruwa da ƙauyuka sama da 200, ana kuma ci gaba da haɓaka harkokin ilimi, kiwon lafiya, wutar lantarki, noma da kuma samar da haɗin kai. Ayyukan Da Suka Game Mutane Babu ayyukan da Oyebanji ya yi fiye da na abubuwan more rayuwa. Sabbin hanyoyi kamar Ikere zuwa Igbara zuwa Odo, Ogotun zuwa Ikogosi, Isinbode zuwa Ara...
    ‘Yan sandan kasar Ghana sun sanar da cewa tserato da wasu ‘yan Najeriya 57 da aka yi faskwaurinsu, haka nan kuma wasu mutane 5 da suke aikata laifuka ta hanyar sadarwar na “Internet” Jami’an ‘yan sandan sun kwace nau’ra mai kwakwalwa 77 da wayoyin hannu 38, sai kuma wasu motoci 2, akwatin talbijin 3, da kuma wasu na’urori da suke amfani da su a yaudarar mutane. A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an ‘yan sandan kasar ta Ghana su ka sanar da kai farmakin a birnin Accra a ranar Laraba 22 ga watan nan na Oktoba. Shekarun mutanen da ake amfani da su wajen yaudarar mutane ta hanyar internet suna a tsakanin 18 zuwa 26,tuni kuma an kai su...
    Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya sanar da bayar da tallafin naira miliyan ɗaya ga duk iyalin da ya rasa ɗan uwa a gobarar tankar man da ta faru a garin Essa, Karamar Hukumar Katcha. Haka kuma, ya ba da tallafin naira dubu ɗari biyar ga kowanne daga cikin waɗanda suka jikkata a lamarin. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai yankin da abin ya shafa, inda ya tantance tare da ganawa da shugabannin al’umma da mazauna yankin. Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027 NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas? Wannan sanarwa ta fito ne daga Sakataren...
    Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da kawi karshen tattaunawa da kasar Canada dangane da batun kasuwanci Shugabann a kasar Amurka ya  zargi Canada da yin amfani da kalmomin tsohon shugaban kasar Amurka Ronald Regan ta hanayar da ba ta dace ba a cikin wasu tallace-tallace akan kudaden fito, inda ya bayyana cewa; ” Saboda  la’akari da halayyarsu an kawo karshen tattaunawar kasuwanci da kasar Canada.” Shugaban kasar na Amurka ya ci gaba da cewa; Cibiyar Ronald Ragan ta sanar da cea, Canada ta murguda zancen Regan yana Magana akan illolin kudin fito, kuma an yi hakan ne domin yin tasiri a cikin matakin da kotun koli ta Amurka za ta dauka akan batun da ake jiran ta fitar...
    MDD ta bayyana cewa a tsakanin kowadanne mutanen Gaza  4, daya daga cikinsu yana fama da yunwa. Mai Magana da yawun kungiyar Agaji ta tarayyar turai, May Musa Sayegh, ta yi ta’aliki akan wannan adadin na masu fama da yunwa a Gaza, inda ta ce; Wannan shi ne hakikanin abinda yake faruwa a kasa, kuma ya shafi mata manya da ‘yan mata da kuma kananan yara masu yawa.” May Musa Sayegh ta fada wa tashar talabijin din aljazira cewa; Sakamakon hare-hare na tsawon shekaru biyu da kuma rashin samun damar shigar da kayan agaji,musamman a arewacin Gaza aka fada cikin wannan halin. Sayegh ta kuma ce; ta fuskar kiwon lafiya, al’amurra suna kara tabarbarewa, domin mutane suna rayuwa cikin bakin...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala October 24, 2025 Manyan Labarai Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano October 24, 2025 Manyan Labarai Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu October 24, 2025
    Kungiyar ‘yan wasan kokawar Iran na gargajiya na matasa ‘yan kasa da shekaru 23, ta lashe kambun duniya bayan da ta samu lambobin yabo mafi yawa. Kungiyar ta Iran ta sami lambobin zinariya 3, da azurfa 1 da kuma tagulla 2. ‘yan wasan da Iran da su ka sami kyautar zinariyar sun hada Iman Muhammadi mai ajin nauyi kilio 72, da Gulam Ridha Farakhi mai ajin nauyi kilo 87 da kuma Fardin Hidayati mai ajin nauyi 130. Wanda ya  sami azurfa kuwa shi ne Sajjad Abbaspur mai ajin nauyi kilo 60, sai kuma wadanda su ka sami tagulla da su ne Ahamd Ridha Muhsin Najad mai ajin nauyi 67,sai Abul Fadal Muhmadim ai ajin nauyi 82. Kungiyar ta Iran ta...
    “Shirin gwamnan na aiwatar da sabon tsarin albashi duk da ƙalubalen tattalin arziki ya nuna tausayinsa, gaskiya, da girmama kimar ma’aikata,” in ji shugabannin kungiyoyin.   Kungiyoyin sun kuma yaba da kokarin gwamnatin wajen gyara da inganta fannonin ilimi da kiwon lafiya inda suka bayyana gyaran da sabunta azuzuwan karatu a dukkan kananan hukumomi 23, amincewa da tsarin ritaya bayan shekaru 65 ko shekaru 40 na aiki ga malamai, da kuma dawo da sama da naira miliyan 500 na ajiyar ( ENDWELL) da aka rike a baya, a matsayin muhimman nasarori.   Ma’aikatan sun kara jinjina wa dawowar tsarin biyan gudunmawar adashin gata na malaman makaranta wato (ENDWELL) na kowane wata, inda suka bayyana cewa tsarin yana taimakawa wajen inganta...
    Ɗan takarar jam’iyyar adawa a zaɓen shugaban ƙasar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary wanda ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen, ya shaida wa BBC cewa a shirye yake ya kare abin da ya bayyana “nasara ƙarara” da ya samu. Yayin da al’ummar ƙasar ke ci gaba da dakon sakamakon zaɓen da za a bayyana a ranar Litinin mai zuwa, Bakary, wanda shi ma tsohon jami’in gwamnatin Paul Biya ne, ya ce zai amince ne kawai da sakamako na gaskiya. Wannan kalami nasa dai zai ƙara rura wutar zaman ɗarɗar da ake yi a ƙasar ta yankin tsakiyar Afirka. Tun daga farkon makon nan ne mutane, musamman magoya bayan Bakary suka riƙa fita kan tituna domin yin gangamin kira...
    Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa matasa dubu ɗaya (1,000) za su samu horo kan tsaron yanar gizo (cyber security) da fasahar binciken dijital (digital forensics) ta hanyar Cibiyoyin Koyon Fasahar Dijital ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) a Jihar Nasarawa. Uwargidan Shugaban Ƙasan ta bayyana haka ne yayin bikin kaddamarwa da miƙa Cibiyar Koyon Fasahar Dijital (Digital Learning Center) a Lafia da wasu jihohin ƙasar. Sanata Oluremi Tinubu ta ce, shirin horon matasan wanda za a rika gudanarwa a kowane mako daga yanzu har zuwa watan Disamba na shekara mai zuwa, yana da nufin yakki da laifukan yanar gizo (cyber crimes) da kuma ƙarfafa matasa su samu ƙwarewa ta yadda za su dogara da kansu a...
    Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ƙara zuba jari a manyan cibiyoyin ilimi domin shirya ɗalibai su zama masu iya fafatawa a matakin duniya. Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne a yayin bikin karrama masu kammala karatu na shekara ta 40 na Jami’ar Ilorin (UNILORIN) da ke Ilorin, Jihar Kwara. A jawabinsa, wanda Shugaban Jami’ar Fasaha ta Tarayya Akure (FUTA), Farfesa Temidayo Oladiji, ya karanta a madadinsa, Shugaba Tinubu ya yi alkawarin ƙarfafa ƙirƙira, bincike, da ilimin da ke gina ƙwarewa (skill-based education) a dukkan jami’o’in Najeriya. Ya yaba wa jami’ar bisa tsayin daka da ladabi da kuma ingancin ilimi da ta dade tana nunawa tun daga kafuwarta. Shugaban Ƙasan ya kuma sanar da cewa Jami’ar...
    Uwargidan Shugaban Ƙasa ta Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da Dijital E-Learning Library a Gusau, Jihar Zamfara — ɗaya daga cikin jihohi goma da aka zaɓa a faɗin ƙasar domin aiwatar da wannan muhimmin aiki ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) tare da haɗin gwiwar Hukumar bunkasa ayukkan fasaha ta kasa (NITDA). A yayin bikin kaddamarwar, Sanata Tinubu ta bayyana cewa wannan aiki ba wai game da fasaha da kwamfuta kawai ba ne, amma yana nufin ƙarfafa matasa, rage gibin fasaha (digital divide), da kuma buɗe sabbin ƙofofin ilimi da ƙirƙira ga al’ummar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya. Uwargidan Shugaban Ƙasa, wacce Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta wakilta, ta bayyana cewa ilimi shi ne...
    Gwamnatin Jihar Sokoto ta amince a rika sauya kuɗaɗe da aka ware wasu wurare zuwa swasu idan can ya fi na farko amfani ga al’umma (virement) na naira biliyan 526 a cikin kasafin kuɗin shekarar 2025. Shugaban taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 12 na bana, Gwamna Ahmad Aliyu, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri wajen gina Jihar Sokoto mai ingantaccen tattalin arziki ta hanyar aiwatar da muhimman sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaban al’umma. Gwamna Aliyu ya bayyana cewa wannan sauyin kasafi an tsara shi ne domin ƙarfafa zuba jari a fannoni masu muhimmanci kamar gina manyan ayyukan raya kasa, inganta ayyukan jin kai, da haɓaka tasirin gudanar da ayyuka — ba tare da ƙara girman...
    Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano. Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano. A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar. Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar. Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin...
    Shirin karfafa ilimin ‘ya’ya mata a jihar Kano ya shirya taron tattaunawa da malamai da limaman masallatan Juma’a domin ƙarfafa haɗin gwiwa da shugabannin addini wajen inganta goyon bayan al’umma ga ilimin ’yan mata a fadin jihar. Taron, wanda yake ɗaya daga cikin dabarun haɗin kai na masu ruwa da tsaki na AGILE, yana da nufin ƙara samun damar karatu, tsayawa da kuma kammala karatun ’yan mata ta hanyar daidaita ayyukan shirin da dabi’u da imanin al’umma. A jawabinsa, Shugaban Shirin AGILE na Jihar Kano, Malam Mujtapha Aminu, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin fayyace wasu rashin fahimta da ake da su game da shirin, da kuma tabbatar da fahimtar juna tsakanin shugabannin addini. A cewarsa, “Shigar malamai...
    Majalisar Tattalin Arzikin Ƙasa (NEC) ta amince da shirin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu na sake fasalin da kuma zamanantar da cibiyoyin horar da jami’an tsaro a faɗin ƙasar. Wannan mataki ya biyo bayan taron majalisar na 152 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda Ministan Tsare-tsaren Kasafi da Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya gabatar da jawabi kan dabarun cimma burin Shugaban Ƙasa na samar da tattalin arzikin da ya kai darajar dala tiriliyan guda. An kafa kwamitin da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ke jagoranta don tsara cikakken tsari na gyaran da sabunta cibiyoyin horar da jami’an ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro cikin wata guda. Mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnonin jihohin...
    Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Har ila yau, shirin nan nata Mata A Aikin Noma, ya bai wa matan karkara sama da 20,000 tallafi da horarwa da ƙara samun kuɗin shiga ga iyalai da kuma wadatar da al’umma. Kazalika, shirin Tallafin Ilimi, ya samar wa fiye da ɗalibai 3,000, guraben karatu, kwamfiyutoci da kuma jagoranci na gari. Ga tsofaffi kuma, Asusun Tallafa wa Tsofaffi ya bai wa tsofaffi 5,000 alawus-alawus da kula da lafiyarsu tare kuma da maido da martabar musamman waɗanda aka yi watsi da su, aka kuma manta da su. Lokacin da iftila’i ya afku a Jihohin Filato da Benuwe a tsakiyar 2025,...
    Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal. Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.  A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta. Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na...
    Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal. Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.  A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta. Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na...
    Kazalika, har yanzu batun tsohon shugaban Majalisar Wakilai wato Salisu Buhari, na 1999, na yin amfani da Takardun karatu na bogi da ya yi iƙirarin ya samo daga Jama’iar Toronto, baƙalar na ci gaba da kafa babban misali, a ƙasar. Badaƙalar ta sa, ba ta tsaya nan ba, ya kuma ƙaryar shekarun na haihauwa, domin kawai, ta tsaya takarar siyasa, a wancan lokacin, wanda kuma ya nuna turjiya daga sauka daga muƙamin na nsa duk da ɗimbin hujjojin da suka bayyana a kansa, inda bayan komai ya bayyana ƙarara, ya sauka daga kan muƙamin shugabancin Majlisar a 2000, ya kuma ɓarke da kuka a Majalisar, ya amsa cewar, Takardunsa na bogi ne. Haka ita ma, tsohuwar ministan kuɗi Kemi Adeosun,...