HausaTv:
2025-08-01@19:06:46 GMT

Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa

Published: 26th, February 2025 GMT

Sojojin kasar Iran sun kammala atisayen hadin giuwa mai suna Zolfaghar 1403 a jiya Talata tare da faretin sojojin Ruwa na kasar.

Atisayen ya hada sojojin sama da na ruwa ne, saboda jarraba yadda bangarorin biyu zasu yi aiki tare a lokacin yaki, duk da cewa ko wani bangare yana aiki a inda ya kore, ya ke kuma da masaniya a kansa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, sojojin zasu hada kai don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu cikin ruwa da kan tudu tare.

Manya-manyan kwamandojin sojojin kasar wadanda suka hada da Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin babban kwamnadan sojojin kasar a bangaren tsare-tsare. Da kuma Manjo Janar Abdulrahim Musavi babban kwamandan sojojin kasar iran.

Atisayen ya hada rawar daji a karkashin ruwa don gwada aiki da makamai, da kuma tudun ruwa shi ma don gwada makaman da ake da su. Sannan da yadda za’a yi rundunonin su yi aiki tare, idan bukatar haka ta taso.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta a Ƙaramar Hukumar Yauri ta Jihar Kebbi a wani mataki don bunƙasa harkokin tsaron iyakokin ruwa.

Hakan na zuwa ne bayan da wata tawagar manyan jami’an sojojin ruwan suka kai ziyara gidan gwamnatin Jihar Kebbi.

Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta  ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa

Sojojin sun kai ziayarar ne ƙarƙashin jagorancin Rear Admiral Patrick Nwatu – wanda ya wakilci babban hafsan sojin ruwan ƙasar.

Rundunar ta ziyarci Kebbi ne domin duba yadda za ta samar da sansaninta a jihar.

Patrick Nwatu ya yi tir da harin ta’addanci a kogin Neja, yana mai cewa yankin ya zama maɓoyar masu safarar makamai da sauran masu aikata laifuka.

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ce ta kammala shirye-shiryen kafa sansanin sojin ruwa a garin Yauri da ke jihar.

Babban Hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla ne ya bayyana hakan a wata ziyarar ban girma da suka kaiwa Gwamnan Kebbi, Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

Da yake jawabi yayin ziyarar, jagoran tawagar Rear Admiral Patrick Nwatu, ya ce ziyarar wani ɓangare ne na faɗaɗa dabarun teku na sojojin ruwan Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi
  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa