Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa
Published: 26th, February 2025 GMT
Sojojin kasar Iran sun kammala atisayen hadin giuwa mai suna Zolfaghar 1403 a jiya Talata tare da faretin sojojin Ruwa na kasar.
Atisayen ya hada sojojin sama da na ruwa ne, saboda jarraba yadda bangarorin biyu zasu yi aiki tare a lokacin yaki, duk da cewa ko wani bangare yana aiki a inda ya kore, ya ke kuma da masaniya a kansa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, sojojin zasu hada kai don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu cikin ruwa da kan tudu tare.
Manya-manyan kwamandojin sojojin kasar wadanda suka hada da Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin babban kwamnadan sojojin kasar a bangaren tsare-tsare. Da kuma Manjo Janar Abdulrahim Musavi babban kwamandan sojojin kasar iran.
Atisayen ya hada rawar daji a karkashin ruwa don gwada aiki da makamai, da kuma tudun ruwa shi ma don gwada makaman da ake da su. Sannan da yadda za’a yi rundunonin su yi aiki tare, idan bukatar haka ta taso.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.
Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.
Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.
Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.
Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.
Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.
Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.
Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata, wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.
Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.
Daga Abdullahi Tukur