Leadership News Hausa:
2025-05-31@09:15:21 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza

Published: 26th, February 2025 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza

A ranar 25 ga wata ne zaunannen wakilin kasar Sin a majalisar dinkin duniya Fu Cong, ya bayyana a taron kwamitin sulhu na MDD game da batun Isra’ila da Falasdinu cewa, tilas ne a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza baki dayanta, don tabbatar da tsagaita wuta mai dorewa. Ya kuma yi kira ga Isra’ila da ta dakatar da aikin soji a yammacin gabar kogin Jordan.

Fu Cong ya bayyana cewa, dole ne mulkin Gaza bayan yakin ya bi ka’idar “Falasdinawa su yi mulkin Falasdinu”, kuma ya kamata kasashen duniya su ba da goyon baya ga sake gina Gaza. Kana kasar Sin ta yi kira ga al’ummomin kasa da kasa da su kara himma wajen kira ga samar da mafita ta siyasa ta kafa kasashe biyu da kuma ba da tabbacin da ya dace da hakan. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

Shugaban kwamitin kungiyar Tarayyar Afrika (AU) Mahmoud Ali Youssouf, ya nanata godiyar kungiyar bisa irin goyon bayan da kasar Sin ke ba ta da ma kasashen Afrika a muhimman bangarori kamar na cinikayya da raya ababen more rayuwa da aikin gona da kiwon lafiya da bunkasa kwarewar jami’ai.

Wata sanarwa da aka fitar jiya Laraba, ta ruwaito Mahmoud Ali Youssouf na bayyana haka ne yayin da yake bankwana da Hu Changchun, shugaban tawagar kasar Sin a AU.

Shugaban na kwamitin AU ya kuma yaba wa jajircewar Hu tare da gode wa kasar Sin dangane da gudunmuwar da ta bayar na gina Cibiyar Kandagarki da Dakile Yaduwar Cututtuka ta Afrika, da taimakonta ga aikin wanzar da zaman lafiya da sauran taimakon da take bayarwa a sauran muhimmman bangarori da suka shafi jama’a a fadin nahiyar Afrika.

Jami’an biyu sun kuma waiwayi nasarorin da aka samu karkashin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika da ya gudana a Beijing a shekarar 2024 tare da bayyana hadin gwiwar AU da Sin a matsayin misalin cudanyar bangarori daban daban. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
  • Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
  • An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
  • An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 
  • AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
  • Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku
  • Duniyarmu A Yau: Wasikar Lawyoyi 800 Ga Firay Ministan Kasar Burtaniya Kan Gaza
  • Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci