Araghchi : Iran Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da Amurka Bisa Matsin Lamba
Published: 26th, February 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa ba zata shiga wata tattaunawa da Amurka ba kan shirinta na nukiliya bisa matsin lamba.
Ministan harkokin wajen Iran ne Abbas Araghchi ya bayyana hakan, inda yake cewa muddin fadar White House ba ta janye matsin lamba wa kasar ba, babu wata tattaunawa.
“A kan tattaunawar nukiliya, matsayin Iran a bayyane yake: ba za mu yi shawarwari cikin matsin lamba, barazana, da takunkumi ba.
“Saboda haka,” in ji ministan harkokin wajen Iran, “babu yuwuwar yin shawarwari kai tsaye tsakaninmu da Amurka kan batun nukiliya matukar dai ana ci gaba da yin amfani da mafi girman matsin lamba a yadda take a halin yanzu.”
Misra Araghchi ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai da takwaransa na Rasha, Sergey Lavrov da ke ziyara a Tehran.
Ministan harkokin wajen kasar ya ce Iran za ta magance batun nukiliyar tare da hadin gwiwa da kawayenta – Rasha da China.
A nasa bangare da yake bayyani game da shirin nukiliyar Iran, Lavrov ya ba da fifiko kan hanyar diflomasiyya.
“Mun yi imanin cewa har yanzu akwai karfin diplomasiyya don warware batun nukiliyar Iran, kuma muna fatan za a iya samun mafita. Ba Iran ce ta haifar da wannan rikicin ba.” Inji shi.
Iran dai ta dade tana fuskantar takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata kan ayyukanta na nukiliya, da batun kare hakkin bil’adama, da dai sauransu, saidai zuwan Donald Trump, ya kara dagula al’amuran inda ya sha alwashin matsin lamba kan kasar ta Iran, domin ta mika wuya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa
Kakakin majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa kyale HKI wanda kasashen duniya suka yi ne, ya ke bawa HKI karfin giwan ci gaba da abinda take yi a gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokokin wanda ake gudanarwa a halin yanzu a birnin Geneva.
Wannan dai shi ne taron shuwagabannin majalusun dokoki na duniya karo na 6 wanda MDD take daukar nauyinta.
Dangane da hare-haren da HKI da Amurka suka kaiwa kasar Iran a cikin watan Yunin da ya gabata kuma ,Qalibof ya bayyana cewa manufarsu it ce lalata shirin Nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya, kwata-kwata. Alhali hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA tana sanya iado a kan ayyukan sarrafa uranium da kasar take yi.
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren kwanaki 12 wanda wadan nan kasashe biyu wadanda basa son zaman lafiya a Iran sun kai mutane kimani 1100 ga shahada. Sannan sun sanya shirin nukliyar kasar Iran cikin hatsari, wanda ya tilasta mana daukar matakai don kare shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci