An Yi Ganawa A Tsakanin Ammar Hakim Na Iraki Da Shugaban Kasar Masar Abdufttah Al-Sisi
Published: 25th, February 2025 GMT
Shugaban kungiyar ‘al-Hikimah” na kasar Iraki Ammar Hakim ya gana da shugaban kasar Masar Abdulfattah al-sisi. A yayin ganawar Ammar Hakim ya jaddada muhimmancin taimaka wa kokarin da Masar take yi na ganin an hana korar falasdinawa daga yankunansu zuwa wajen Falasdinu.
Ammar Hakim ya kuma ce, a yayin wannan ganawar na bayyana wa shugaban kasar jinjinawarmu akan yadda Masar ta kasance mai taimaka wa Falasdinawa.
Haka nan kuma mun nuna goyon bayanmu ga kokarin Masar al’umma da gwamnati na hana tilasatawa Falasdinawa yin hijira da kuma kare hakkokin Falasdinawa da riko da kasarsu.
Har ila yau Ammar Hakim ya ce ganawar tasu ta tabo batutuwa da su ka shafi halin da ake ciki a wannan yankin da kuma wajabcin aiki a tsagaita wutar yaki a yankin Gaza.
Sayyid Ammar Hakim ya kuma yi ishara da muhimmanci sake gina yankin na Gaza ba tare da an fitar da mazaunansa daga ciki ba. Bugu da kari bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci kafawa Falasdinawa daularsu akan iyakokin 1967 da birnin Kudus zai zama babban birninta domin haka ne hanyar samar da zaman lafiya a cikin wannan yankin.
Akan halin da ake ciki a matakin wannan yankin kuwa, Sayyid Ammar Hakim ya ce; Kasar Iraki tana son ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin da kuma warware sabanin da ake ciki a wannan yankin da kusanto da fahimtar juna a tsanakin bangarori mabanbanta.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ammar Hakim ya wannan yankin
এছাড়াও পড়ুন:
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Ofishin kula da zirga-zirgar kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin ya ce, an harba kumbon Shenzhou-21 mai dauke da ‘yan sama jannatin kasar Sin 3 cikin nasara, a daren jiya Juma’a, agogon Beijing.
Daga baya kumbon ya sarrafa kansa wajen hade jikinsa da na tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, ta yadda ‘yan saman jannatin suka shiga tashar, inda tsoffin ‘yan saman jannati 3 da suka dade a cikin tashar, suka yi musu maraba. Hakan ya shaida haduwar sabbi da tsoffin ‘yan sama jannatin kasar Sin karo na 7 a tashar binciken sararin samaniya ta kasar.
Bisa shirin da aka yi, wadannan ‘yan sama jannati 6 za su kwashe kimanin kwanaki 5 suna aiki tare a cikin tashar, kafin tsoffin ‘yan saman jannatin 3 su kama hanyar dawowa gida.
Zuwa yanzu, kasar Sin ta riga ta tura ‘yan sama jannati 44 zuwa sararin samaniya. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA