HausaTv:
2025-08-01@13:37:16 GMT

Tawagar Iran a Beirut ta gana da shugabannin Lebanon

Published: 24th, February 2025 GMT

Tawagar gwamnatin Iran da ke ziyara a birnin Beirut domin halartar jana’izar shugabannin gwagwarmaya Sayyed Hassan Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine karkashin jagorancin shugaban majalisar dokokin kasar Mohammad Bagher Ghalibaf da ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi sun gana da shugaban kasar Labanon Joseph Aoun.

Bayan nan kuma tawagar ta gana da shugaban majalisar dokokin kasar Nabih Berri, sannan ta ci gaba da tattaunawa da sauran jami’ai da suka hada da firaministan kasar Labanon Nawaf Salam.

Ghalibaf da sauran jami’ai sun tafi kasar Lebanon a safiyar Lahadi don halartar jana’izar Sayyid Hassan Nasrallah, tsohon babban sakataren kungiyar Hizbullah, da kuma magajinsa  Sayyed Hashem Safieddine, wadanda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kashe su a karshen shekarar da ta gabata.

Da yake zantawa da manema labarai gabanin tafiyar tasa, Ghalibaf ya bayyana jana’izar a matsayin wani lokaci mai ma’ana ga kungiyar gwagwarmaya, duniyar musulmi, da kuma al’ummar Lebanon.

A lokacin da ya isa birnin Beirut babban jami’in na Iran ya bayyana Nasrallah a matsayin wani mutum mai babban matsayi kuma abin alfahari ga duniyar musulmi, yana mai jaddada abin da ya bari a matsayin wata alama ta tsayin daka a kan yakin kisan kare dangi na “Isra’ila” a Gaza.

Ghalibaf ya kara da cewa, duk da shahadarsu, amma Hizbullah da al’ummar Lebanon na alfahari da wadannan gwaraza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba

Kakakin dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran “IRGC” ya bayyana cewa: Hasashen Raunin Iran ya gushe, kuma ba zai sake dawowa ba

Kakakin dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Ali Mohammad Na’eini ya jaddada cewa: Ra’ayin cewa Iran mai rauni ce ya raguje kwata-kwata, yana mai jaddada cewa; Yakin kwanaki 12 na baya-bayan nan ya fallasa gazawar makiya wajen karya manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, sannan kuma ya nuna cewa duk wani sabon harin wuce gona da iri zai fuskanci martani mai tsanani da gauni da zai wurga makiya cikin mummunar nadama.

Hakan ya zo ne a jawabin da Birgediya Janar Na’eini ya gabatar a jiya Laraba a wajen bikin tunawa da shahidi Ramadan Ali Jobadari da shahidan yakin baya-bayan nan. Ya kara da cewa: “Babban bangare na yakin kwanaki goma sha biyu ya kasance yakin kafar watsa labarai da na kwakwalwa da kuma fahimtar hakikanin juna,” ya kara da cewa, “Sun samu gagarumar nasara a fagen yada labarai a lokacin yakin da aka yi a baya-bayan nan. Da kafofin watsa labaru ba su da tasiri, da makiya ba su kai hari kan kafofin watsa labaru da ‘yan jarida ba.

Ya bayyana cewa, “a cikin wannan yakin, makiya sun kai hare-hare kan manyan cibiyoyin kasa da suka hada da cibiyoyin kimiyya da na masana, kwamandojin soji, hedkwatar gudanarwa, cibiyoyin leken asiri da tsaro, da kuma kafofin watsa labarai a matsayin cibiyar tsara labarin.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa