Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya Yi Fatali Da Zargin Australia A Kan Atisayen Sojojin Kasar
Published: 23rd, February 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin ya yi Allah wadai da kasar Australia bisa yadda ta zargi kasar Sin da yin atisayen soja bisa doka a tekun dake kusa da kasar ta Australia.
Kakakin, Wu Qian ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyin kafofin watsa labaru game da zargin na Australia cewa jiragen ruwan yaki uku na kasar Sin sun yi atisayen soja a tekun dake kusa da kasar Australia.
Wu Qian ya bayyana cewa, zargin da kasar Australia ta yi ba shi da tushe balle makama, domin yankin tekun da jiragen ruwan yakin na kasar Sin suka yi atisayen soja yana can nesa da layin teku na kasar Australia, kuma yanki ne da ba ya cikin mallakar wata kasa. Kakakin ya kara da cewa, kafin lokacin, sai da kasar Sin ta ba da sanarwa sau da dama a kan gudanar da atisayen, sai dai kuma abin mamaki, bayan da jiragen ruwan yakin kasar suka harba boma-bomai zuwa tekun, sai Australiya ta yi zargin.
Ya ce, Sin ta gudanar da ayyukan atisayen bisa dokokin kasa da kasa da ka’idojin zirga-zirga na kasa da kasa, wadanda ba za su kawo illa ga tsaron zirga-zirgar jiragen sama ba. Kuma kasar ta Australia ta san lamarin, amma kuma ta zargi kasar Sin da abin da ba shi da tushe balle makama, kuma Sin tana nuna rashin jin dadinta game da batun. (Zainab Zhang)
কীওয়ার্ড: kasar Australia
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
A yau Asabar ne kasar Sin ta yi nasarar harba tauraron dan Adam na lura da yanayin bala’u a doron kasa, wanda ake sa ran zai rika samar da bayanai ga kasar Sin dangane da aukuwar bala’u daga indallahi, ta aikewa da sakwanni tsakanin sararin samaniya zuwa doron duniya.
An harba tauraron dan Adam din mai suna Zhangheng 1-02, ta amfani da rokar Long March-2D, daga tashar harba kumbuna ta Jiuquan dake arewa maso yammacin kasar Sin, da karfe 4 saura mintuna 4 agogon Beijing, ya kuma shiga da’irarsa ba tare da wata matsala ba, kamar dai yadda hukumar kula da binciken sararin samaniya ta kasar Sin ko CNSA ta tabbatar.
Kazalika, CNSA ta ce, wannan aiki muhimmin mataki ne da Sin ta taka, a turbar nazarin yanayin doron kasa na zahiri. An sanyawa tauraron sunan wani shahararren mai kirkire-kirkire na kasar Sin, wato marigayi Zhang Heng, wanda shi ne mutum na farko a duniya, da ya kago na’urar “seismoscope” ta hasashen aukuwar girgizar kasa, shekaru sama da 1,800 da suka gabata, kuma an samar da tauraron ne da hadin gwiwar Sin da kasar Italiya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp