Aminiya:
2025-05-01@00:46:41 GMT

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Obi

Published: 21st, February 2025 GMT

Dan takarar shugaban ƙasa a Jam’iyyar Leba (LP) a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce Najeriya ta daɗa taɓarɓarewa fiye da lokacin da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja Ibrahim Badamasi Babangida ya bar mulki a shekarar 1992.

Obi ya bayyana haka ne a lokacin da yake tsokaci kan ƙaddamar da littafin tarihin Babangida da aka daɗe ana jira, mai suna ‘A Journey in Service’.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno

Aminiya ta gano cewa, ba a ba wa Obi damar shiga ba cikin zauren taron ƙaddamar da littafin ba, tare da wasu da dama da aka yi zauren taro na Congress Hall a otal din Transcorp Hotel, inda aka gudanar da taron saboda an kulle ƙofofin shiga bayan isowar Shugaba Bola Tinubu.

Obi, a saƙonsa da ya wallafa a shafin sada zumunta na X, ya bayyana cewa irin gudunmawar da IBB ke bayarwa ga tattalin arzikin Najeriya da gagarumin goyon bayansa ga harkokin kasuwanci da bunƙasar kamfanoni masu zaman kansu ba su da iyaka.

Da yake magana a kan abin da ya kira wasu muhimman abubuwa guda biyu na jawabin da IBB ya yi game da zaɓen 1993, ya ce Najeriya ba ta ci gaba ba kamar takwarorinta daga 1992 lokacin da IBB ya bar gwamnati.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya

Kalli yadda aka karɓi ’yan Najeriya guda 203 da aka dawo da su daga ƙasar Libya.

(Hoto: Onyekachukwu Obi).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”