Aminiya:
2025-06-15@23:15:05 GMT

EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a Gombe

Published: 20th, February 2025 GMT

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), ta gargaɗi shugabannin ƙananan hukumomi da su guji almundahana tare da yin amfani da kuɗaɗen jama’a bisa gaskiya da adalci.

Shugaban EFCC, Mista Ola Olukoyede ne, ya bayyana haka yayin wani taro da aka shirya a Jihar Gombe kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi.

Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida

A cewarsa, samun ‘yancin cin gashin kai ba yana nufin cewa shugabannin ƙananan hukumomi ba za a iya hukunta su ba idan sun aikata ba daidai ba.

“Shugabannin ƙananan hukumomi ba su da kariya a tsarin mulkin ƙasa. Idan aka samu rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a, dole ne a ɗauki mataki,” in ji Olukoyede.

Ya kuma bayyana cewa EFCC za ta ƙara tura jami’anta zuwa Jihar Gombe domin sanya ido kan yadda ake sarrafa kuɗaɗen ƙananan hukumomi.

Har ila yau, Olukoyede ya yaba wa hukuncin Kotun Ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi damar samun cikakken iko kan kuɗaɗensu, inda ya ce hakan zai taimaka wajen inganta ayyukan ci gaba.

Sai dai ya nuna damuwa kan yiwuwar wasu su karkatar da kuɗaɗen da aka ware don ayyukan al’umma.

Ya yi kira ga shugabannin ƙananan hukumomi da su bi doka wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a.

“Ku tabbatar da gaskiya a dukkanin ayyukanku, ku kuma san dokokin da suka shafi amfani da kuɗaɗen jama’a. Rashin sanin doka ba hujja ba ce,” ya gargaɗe su.

Taron, wanda aka yi wa take da “’Yancin Cin Gashin Kai na Ƙananan Hukumomi: Samar da Ci Gaba Mai Ɗorewa,” ya mayar da hankali ne kan yadda ake iya amfani da kuɗaɗen jama’a ta hanyoyin da za su amfanar da al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargaɗi Ƙananan Hukumomi amfani da kuɗaɗen jama a

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba
  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran