’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
Published: 20th, February 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe wasu ’yan kasuwar Gwari 12, tare da sace wasu yayin da suke kan hanyarsu ta komawa Zariya bayan cin kasuwa.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Tafoki da ke Jihar Katsina, bayan ’yan bindigar sun buɗe wa motarsu wuta.
An haramta wa manyan tireloli aiki a Najeriya Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a SakkwatoMasu sana’ar Gwari da abin ya shafa ’yan kasuwar Ɗan Magaji ne daga Ƙaramar Hukumar Zariya, a Jihar Kaduna.
Aminiya ta tattauna da wasu daga cikin waɗanda suka tsira, waɗanda suka ji raunuka, da kuma waɗanda aka sako bayan biyan kuɗin fansa Naira miliyan biyu.
Muhammad Zaharraddeen Sharaihu shi ne mutumin da ya kai wa ’yan bindigar kuɗin fansa domin a sako mahaifinsa da wasu mutum uku da aka yi garkuwa da su a dajin Katsina.
Zaharraddeen, ya ce tun yana kan hanya ‘yan bindigar suka riƙa kiran wayarsa har sai da ya isa inda suka ce ya tsaya.
Daga nan suka umarce shi da ya hau babur, sannan suka ce ya tsaya a wani waje don miƙa musu kuɗin.
Bayan ya miƙa kuɗin, wani mutum ya karɓa daga hannunsa, sannan aka umarce shi da ya koma bakin hanya ya jira fitowar ’yan uwansa.
A cewarsa, tun ƙarfe 1 na rana sai kusan Magariba aka sako mahaifinsa da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su.
Mutum huɗu da aka biya miliyan biyu kafin a sako su sun haɗa da Malam Sharihu Umar Shehi, Malam Magaji Idris, Lawal Gambo Kwalano da Ida Ɗan Gwari
Lamarin ya ƙara dagula yanayin tsaro a yankin, inda jama’a ke fargabar ci gaba da ayyukan kasuwancinsu a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan kasuwa Garkuwa Gwari Zariya yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla Falasdinawa 35 dane suka hada da kananan yara aka kashe a wanisabon kisan kiyashi na Isra’ila a zirin Gaza.
A cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza, wadannan hare-haren sun yi sanadin mutuwar mutane 35 tare da jikkata 109 a cikin sa’o’i 24 da suka gabata.
Adadin wadanda sukayi shahada sakamakon yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a yankin da aka yi wa kawanya ya zarce 52,400.
Adadin wadanda suka jikkata kuma ya kai kusan 118,014 tun daga watan Oktoban 2023.
Majalisar Dinkin Duniya dai ta yi gargadin barkewar ayyukan jin kai a Gaza.
Hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) ta fitar da wani kakkausan gargadi game da matsalar jin kai da ke kara tabarbarewa a Gaza a dai dai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-haren bama-bamai da kuma killace fararen hula da ke fama da yunwa.
Tun cikin watan Maris ne Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya haramta kai kayan agaji zuwa Gaza, a wani mataki da ya ce na da nufin tursasa Hamas ta amince da tsawaita matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila.