Leadership News Hausa:
2025-09-18@05:29:10 GMT

Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta

Published: 20th, February 2025 GMT

Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta

Hamas ta nuna shirin ta na sakin duk sauran fursunonin da take riƙe da su Gaza a cikin musanye guda cikin mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninnta da Isra’ila.

Babban Jami’in Hamas, Taher al-Nunu, ne ya bayyanawa masu shiga tsakani cewa ƙungiyar tana da niyyar sakin fursunonin gaba ɗaya maimakon rarraba su kashi-kashi kamar yadda aka yi a mataki na farko, wanda ya ce tabbaci ne da kuma shirinsu na ci gaba da warware batun.

Isra’ila Ta Fara Sakin Fursunonin Falasɗinawa 369, Ciki Har Da Waɗanda Aka Yanke Wa Hukuncin Ɗaurin Rai Da Rai Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

A ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wutar na yanzu, an saki fursunonin Isra’ila 19 a madadin fiye da Falasdinawa 1,100 da ke gidajen yari, wanda a yanzu fursunoni 58 ne za su rage a Gaza, sannan ana shirin mayar da gawarwakin fursunoni takwas da suka mutu cikin matakai biyu.

Ana sa ran mataki na biyu na yarjejeniyar zai fayyace matakan da za a ɗauka domin cimma cikakken tsagaita wuta, inda ake shirin fara tattaunawa a wannan mako.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Daga ranar 14 zuwa 15 ga wata, an gudanar da sabon zagayen shawarwari kan harkokin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka a birnin Madrid, babban birnin kasar Spaniya, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra’ayoyi a kan harkokin cinikayya da ke janyo hankalinsu, tare da cimma daidaito ta fannin daidaita batutuwan da suka shafi Tiktok, da rage shingayen zuba jari, da sa kaimin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu.

Taron shawarwarin ya kasance zagaye na hudu da sassan biyu suka gudanar cikin watanni biyar da suka wuce. Kwatankwacin shawarwarin da aka gudanar a baya, a karo na farko, an sanya Tiktok cikin batutuwan da aka tattauna a shawarwarin na wannan zagaye. Yadda Sin da Amurka suka cimma daidaito a kan batun, ya kuma sake shaida cewa, samun moriyar juna shi ne tushen huldar kasashen biyu ta fannin tattalin arziki da cinikayya.

Hada karfi da karfe shi ne mafita daya tilo, a yanayin da ake ciki na karancin karfin bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Ba za a rasa samun sabanin ta fannin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka ba, amma duk da haka, akwai mafita idan sun dinga yin shawarwari da juna. A gaba, ya kamata sassan biyu su tabbatar da daidaito da shugabannin kasashen biyu suka cimma, musamman ma ya kamata Amurka ta samar da yanayin kasuwanci mai adalci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da Tiktok, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, don su kiyaye nasarorin da suka cimma a shawarwarin, don tabbatar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu yadda ya kamata. (Lubabatu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila