HausaTv:
2025-06-15@13:21:01 GMT

Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon

Published: 18th, February 2025 GMT

Dakarun “Kassam” na kungiyar Hamas sun sanar da shahadar Muhammad Shahin wanda daya ne daga cikin kwamandojinta da ya yi shahada sanadiyyar harin da HKI ta kai masa a birnin Saida na kasar Lebanon.

Sanarwar ta dakarun “Kassam” ta ce, Muhammad Ibrahim Shahin wanda ake yi wa lakabi da Abul-Bara’a ya yi shahada ne a karkashin “Tufan-ak-Aksa” bayan da ‘yan mamayar HKI su ka yi masa kisan gilla a garin Saida dake kudancin Lebanon a jiya Litinin.

Har ila yau dakarun Kassam sun yi bayani akan rawar da shahidin ya taka a fagen gwgawarmaya da jihadi akan ‘yan mamaya, tun daga boren Intifada na Aksa, har zuwa farmakin guguwar Aksa.

Haka nan kuma bayanin na Kassam ya ce, Abul-Baraa ya riski dan’uwansa Shahin Hamzah Shahid wanda ya gabace shi da yin shahada da kuma sauran ‘yan’uwansa shahidai masu tsarki.

Kassam din ta yi alkawalin ci gaba da tafiya akan tafarkin shahidin na jihadi da gwagwarmaya har zuwa cimma manufofin al’ummar Falasdinu na ‘yanto da Falasdinu da fursunonin da suke kurkuku da kuma komawar  Falasdinawa ‘yan hijira zuwa gida.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi Allah wadai da kutsawa cikin masallacin al-Aqsa da ministan Isra’ila Itamar Ben-Gvir ya yi a baya bayan nan, tana mai cewa tana da nufin tayar da “yakin addini” a wannan wuri mai tsarki.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta ce “Kutsen da Itamar Ben-Gvir, ya yi a cikin masallacin Al-Aqsa mai alfarma, da kuma ziyarar tsokanar da ya kai a harabar masallacin… rashin mutunta ra’ayin musulmi da kuma keta alfarma da matsayin masallacin Al-Aqsa a duniyar Musulunci.”

Kungiyar ta jaddada cewa wannan wulakanci da aka yi yana nuna ” girman kai na wannan gwamnati mai tsattsauran ra’ayi da kuma dagewarta na rura wutar yakin addini.”

Hamas ta kuma bukaci dukkanin kasashen Larabawa da na musulmi masu son ‘yanci da su kare  masallacin Al-Aqsa daga fuskantar karuwar kutse.

Ministan na Isra’ila Ben-Gvir tare da wasu gungun ‘yan Isra’ila sun mamaye harabar masallacin Al-Aqsa da ke gabashin Quds da aka mamaye tare da gudanar da ayyukan ibada a harabar masallacin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini