Iran Za Ta Aike Da Tawaga A Matakin Koli Don Halartar Jana’izar Nasrallah
Published: 17th, February 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa za ta aike da tawaga a matakin koli zuwa jana’izar mirigayi babban sakataren kungiyar Hizbollah ta kasar Lebanon Hassan Nasrallah.
Da yake sanar da hakan kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya ce kasar za ta halarci gagarumin bikin mai matukar muhimmanci,
Tunda farko dai kungiyar gwagwarmayar Hizbullah ta kasar Lebanon ta sanar da cewa tawagogin kasashe 79 za su halarci bikin tunawa da marigayi babban sakataren kungiyar Sayyid Hassan Nasrallah da kuma shugaban majalisar zartarwarta Sayyid Hashem Safieddine.
Sheikh Ali Daher, kodinetan babban komitin jana’izar Nasrallah da Safieddine, ya bayyana cewa bikin da aka shirya yi a ranar 23 ga watan Fabrairu, zai kasance “ranar tunawa da shugaban wanda aka zalunta a kan ma’abuta girman kai, da kuma shahidan bil’adama a kan mulkin mallaka”.
Ya kara da cewa jana’izar za ta ci gaba da zaburar da mutane masu ‘yanci a duniya shekaru da dama masu zuwa.”
Daher ya yi nuni da cewa bikin zai dauki kimanin sa’a daya kuma zai hada da jawabin babban sakataren kungiyar Sheikh Naim Qassem.
Sayyid Nasrallah ya yi shahada ne a yayin harin bam da Isra’ila ta kai a kudancin birnin Beirut a ranar 27 ga Satumba, 2024, Shi kuwa Safieddine ya yi shahada a lokacin harin da Isra’ila ta kai a watan Oktoban 2024.
Kungiyar Hizbullah ta dage bikin jana’izar shugabannin biyu saboda fargabar hare-haren Isra’ila a yayin bikin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cikakken shirin Iran na tunkarar duk wani mataki na wuce gona da iri a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar barazanar daukar matakin soji kan kasar.
Manjo Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne yau Alhamis, yayin da rahotanni ke nuni da cewa, Amurka ta sanya ofisoshin jakadancinta da sansanonin sojinta da ke yammacin Asiya cikin shirin ko-ta-kwana saboda fargabar yiwuwar kai wa Iran hari.
“A wasu lokuta makiya suna yi mana barazana da daukar matakin soji, mun sha bayyanawa, kuma muna maimaitawa a yau, cewa mun shirya tsaf don fuskantar duk wani yanayi,” in ji shi.
“Muna da kwarewa, mun karfafa karfinmu tare da samar da dabaru a cikin tsare-tsarenmu.
Muna sa ido sosai kan sojojin abokan gaba kuma mun aiwatar da shirye-shiryenmu.” Inji shi.
Har ila yau babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya gargadi makiya game da duk wani gigi, ya kuma shawarce su da su yi la’akari da illolin da ayyukansu zasu haifar.