Kotu Ta Hana Gwamnatin Tarayya Riƙe Wa Kano Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomi
Published: 17th, February 2025 GMT
“Hakkinmu ne mu tabbatar da cewa kuɗin jama’a ba su faɗa hannun jagorori marasa cancanta ba. Saboda haka, za mu ɗaukaka ƙara kuma mu ci gaba da fafutuka har sai an yi mana adalci,”
in ji shi.
.এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce farin jinin jam’iyyar adawa ta PDP ya dusashe a jihar.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martanin da wasu jam’iyyun adawa suka yi, wajen zargin gwamnatin jihar da rashin bayyana yadda ta ke kashe kuɗaɗen da aka ware wa ilimi, lafiya, da gine-gine.
Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinyaDungurawa, ya ce waɗannan zarge-zargen siyasa ce kawai, ba su da tushe ko makama.
Ya ce waɗanda ke sukar gwamnati su ne suka gaza lokacin da suka yi mulki a Kano.
“Da farko, muna gode musu da suka amince muna aiki. Amma muna tunatar da su cewa sun yi shekara takwas suna mulki amma ba su bar wani abin a-zo-a-gani ba,” in ji Dungurawa.
Ya zargi gwamnatocin baya da yin ayyukan da ba su da tasiri, ba tare da duba buƙatun al’umma ba.
“Misali duba gadar ƙasa da suka yi a Dangi. Ba ta da wani amfani. Babu cunkoso a wajen da zai sa a gina irin wannan. Kawai sun zuba kankare ne ba tare da wata manufa ba,” in ji shi.
Dungurawa, ya ce a ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, gwamnatin NNPP ta mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar gyaran tituna da gina gadoji don sauƙaƙa zirga-zirga a jihar.
“Yanzu haka, ramuka ƙadan za ka ga ni a titunan Kano. Titunanmu sabbi ne, alamomin titi a bayyane suke, fitilun titi suna aiki.
“Wannan yana nuna cewa masu kishin jihar sun karɓi ragamar mulki,” in ji shi.
Ya kuma kare yadda gwamnati ke biyan fansho, inda ya bayyana cewa an riga an biya Naira biliyan 27 daga cikin Naira biliyan 48 da gwamnatin jihar ta gada a matsayin bashi.
“A cikin shekara biyu kacal, mun biya Naira biliyan 27 sannan an biya biliyan 22, kuma za a biya wata biliyan biyar a watan Disamba.
“Wannan ya nuna irin yadda muke tafiyar da gwamnati da gaskiya,” in ji shi.
Game da maganar da wasu ‘yan adawa ke yi cewa jam’iyyunsu na ƙara ƙarfi, Dungurawa ya yi watsi da hakan.
“Wasu daga cikinsu ko a gidajensu ba za a goyi bayansu ba. PDP ba ta da wani ƙarfi. A zahirin gaskiya, mutuwa ta ke ƙara yi. Shugabanninta ba su da haɗin kai kuma son kansa yake yi,” in ji Dungurawa.
Bayan taɓo batun haɗakar ADC, Dungurawa ya ce hakan na nuna rikicin da ke cikin PDP.
“Idan har ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP yana shirin komawa wata jam’iyya, me hakan ke nunawa?
“Yana nuna cewa jam’iyyar ba ta da tsari ko jagoranci. ‘Yan siyasa masu kishin ƙasa sun riga sun bar jam’iyyar tuntuni,” in ji shi.