HausaTv:
2025-11-03@10:01:56 GMT

A Kalla Mutane 48 Ne Su Ka Mutu A Wajen Hako Zinariya  A Kasar Mali

Published: 16th, February 2025 GMT

A jiya Asabar ne aka sami hatsari a wani wurin hako zinariya dake yammacin kasar Mali da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 48.

‘Yan sanda a yankin da lamarin ya faru ne su ka sanar da faruwar hatsarin a wurin da ake hako zinariya ba tare da izinin hukuma ba,wanda kuma ya rutsa da wata mace da karamin yaronta.

Wani jami’in yankin da lamarin ya faru ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne a wani wurin hako zinariya da aka kauracewa,da a halin yanzu mata ne su ka fi hako zinariya a cikinsa.

A nashi gefen shugaban hukumar masu hako zinariya a kasar ta Mali Abubakar Keita ya bayyana cewa; A kalla mutane 48 ne su ka kwanta dama sanadiyyar afkuwar wannan hatsarin.

Daga lokaci zuwa lokaci ana samun afkuwar irin wannan hatsarin  a cikin kasashen yammacin Afirka da ake hako zinariya ba bisa izinin mahukunta ba, kuma ba bisa tsari ba.

Mali tana cikin kasashen da suke da wuraren hako ma’adanai mafi girma a cikin yammacin Afirka wanda yake taka rawa a kasafin kudin kasar da kawo ¼.

A watan Disamba na shekarar da ta gabata, ministan kudi na kasar ta Mali Alosini Sano ya ce, kasarsa ta gudanar da wani bincike da sake yin bitar wata yarjejeniya akan cinikin zinariyar da ya ba ta damar dawo da kudaden da sun kai kudin Farank biliyan 700, wato  fiye da Euro biliyan daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hako zinariya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Labarai Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa