Aminiya:
2025-09-17@23:26:38 GMT

Gwamnatin Zamfara ta haramta taron siyasa saboda tsaro

Published: 16th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Zamfara ta haramta gudanar da tarukan siyasa a faɗin jihar har sai abin da hali ya yi, domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Wannan mataki ya biyo bayan wasu tashe-tashen hankula masu nasaba da siyasa, inda jam’iyyar adawa ta APC ta koka cewa an kai wasu daga cikin jami’anta hari.

Janar Musa ya fallasa ƙasashen da ke ɗaukar nauyin Boko Haram Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida Dalilin Haramta Tarukan Siyasa

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Zamfara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Al’amuran Jama’a, Mustafa Jafaru Kaura, ya bayyana cewa an ɗauki mataki ne, sakamakon wata hatsaniya da ta auku a Ƙaramar Hukumar Maru.

Ya ce: “Daga yanzu, an haramta duk wani taro ko gangami da zai iya haddasa tashin hankali, musamman ganin yadda aka rasa rayuka da ƙone dukiya mai yawa a Ƙaramar Hukumar.”

Ya kuma ƙara da cewa wannan dakatarwa ba ta dindindin ba ce, illa dai mataki ne na wucin gadi domin kiyaye zaman lafiya a jihar.

Martanin Jam’iyyar APC

A nata ɓangaren, jam’iyyar APC reshen Zamfara, ta soki matakin, inda ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne saboda tsoron ƙarfin jam’iyyar a jihar.

Mai magana da yawun jam’iyyar, Malam Yusuf Idris Gusau, ya ce: “Ai abin mamaki ne a ce an hana tarukan siyasa, domin ba gangamin yaƙin neman zaɓe aka shirya ba.

“Babu wata doka da ta hana tarukan jam’iyyu, don haka gwamnati ba ta da hurumin hana mu gudanar da harkokinmu na siyasa.”

Ya ƙara da cewa APC jam’iyya ce mai rijista a ƙasa, kuma mabiyanta suna bin doka ba tare da haddasa wata fitina ba.

Fargabar Ƙarin Tashin Hankali

Ana dai ganin wannan mataki na gwamnati da martanin APC na iya ƙara dagula lamarin siyasa a jihar.

Masana da masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin akwai buƙatar a samu tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu, tare da shiga tsakani da dattawa da jami’an tsaro domin hana rikicin ya tsananta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: martani Siyasa Taruka Zamfara jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025

Gwamnatin Jihar Jigawa  ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.

Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.

Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.

Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar