Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba
Published: 16th, February 2025 GMT
Shekara guda bayan da Hukumar Zabe (INEC) ta dakatar da sake zaben mazabar Tsanyawa da Kunci a Majalisar Dokokin Jihar Kano, yankin ya ci gaba da zama babu zaɓaɓɓen wakili da yake wakiltar su a Majalisar Dokokin jihar.
Hukumar Zabe ta Ƙasa ta dakatar da sake zaɓen ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2024, bayan da wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ce suka tarwatsa sake gudanar da zaben a wasu rumfunan zabe da dama a kananan hukumomin biyu.
A shekarar 2023 ce Kotun Daukaka kara ta soke zaben dan Majalisar Dokoki na Jam’iyyar APC mai wakiltar mazabar, Alhaji Garba Ya’u Gwarmai, biyo bayan kalubalantar nasarar da ya samu a shari’a da Alhaji Yusuf Ali Maigado na Jam’iyyar NNPP ya shigar.
Kotun ta bayar da umarnin a sake yin zabe cikin kwanaki 90.
Da yake tsokaci kan rashin wakilcin da mazabar ta daɗe ba ta da shi, masanin harkokin siyasa, Dokta Kabiru Sufi ya ɗora alhakin lamarin ga Hukumar Zabe ta kasa da kuma ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki daga mazabar, yana mai zargin su da gazawa wajen ganin an gudanar da zaben cikin lumana da kwanciyar hankali.
“Masu ruwa da tsaki a yankin suna da hujjar tambayar Hukumar Zabe ta kasa dalilin da ya sa ta gaza kammala aikin gudanar da zaben kamar yadda doka ta tanada,” in ji Dokta Sufi.
Wani mazaunin yankin Malam Muhammad Tsamiya ya koka da rashin samun wakilci, inda ya bukaci gwamnan jihar da ya tabbatar da cewa ba a yi watsi da mazabar ba, musamman ganin yadda take fama da rashin isassun kayayyakin more rayuwa.
“Kunci yanki ne mai nisa, inda hatta malaman da aka tura domin gudanar da aikin nan sun ki zuwa saboda ba mu da hanyoyi ga matsalar ruwan sha da dai sauran matsaloli.
“Don haka a siyasance, gwamna shi ne wakilinmu tun da jihar baki ɗaya mazabarsa ce,” inji shi.
Ya zuwa yanzu dai Hukumar Zabe INEC ba ta sanar da wata rana ba da za a sake gudanar da zaben ba.
Da wakilinmu ya tuntubi shugabar kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a ta Hukumar Zabe ta Kasa, Hajiya Safiya ta bayyana cewa, idan hukumar ta shirya lokacin gudanar da zaben, kwamishinan Hukumar Zabe ta kasa, Ambasada Abdu Zango zai kira taron masu ruwa da tsaki domin tattauna tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓen.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Zaɓe gudanar da zaben Hukumar Zabe ta
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kano, Alhaji Salim Hashim Idris Gwangwazo, ya kaddamar da shirin kula da ido kyauta domin tallafawa jama’a da ke fama da ‘Glaucoma’ da ke lalata rijiyoyin ido, da ‘Cataract’ wato yanar ido da sauran cututtukan ido.
An gudanar da shirin ne a Asibitin Kwalli tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Hukumar Lafiyar Farko ta Jiha, da ƙaramar hukumar da masu bada tallafi daga kasashen waje.
Shirin ya haɗa da gwaje-gwajen lafiyar ido, da bayar da magunguna da kuma rarraba tabarau kyauta, musamman ga marasa ƙarfi a cikin al’umma.
Shugaban ƙaramar hukumar, ta bakin Kwamishinan Lafiya Alhaji Mustapha Darma, ya bukaci jama’a da su ci gaba da tallafawa gwamnati wajen samar da ingantaccen kulawa.
A baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta dauki nauyin kula da lafiyar ido ga mutum sama da 500 daga Birnin Kano da sauran kananan hukumomi.
Shugaban kula da lafiya am matakin farko na ƙaramar hukumar, Alhaji Lawan Jafar, ya ce wadanda lalurar su ba ta tsananta ba za a ba su shawarwarin kula da lafiyar su, da magunguna, wa su ma har da tabarau, yayin da wadanda ta su ta tsananta kuma za a musu tiyata.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun nuna godiya tare da yi wa gwamnati addu’a don samun nasara.
Shugaban tawagar likitocin, Dr. Kamal Saleh, ya tabbatar da cewa shirin ya samu nasara sosai.
Daga Khadijah Aliyu