Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba
Published: 16th, February 2025 GMT
Shekara guda bayan da Hukumar Zabe (INEC) ta dakatar da sake zaben mazabar Tsanyawa da Kunci a Majalisar Dokokin Jihar Kano, yankin ya ci gaba da zama babu zaɓaɓɓen wakili da yake wakiltar su a Majalisar Dokokin jihar.
Hukumar Zabe ta Ƙasa ta dakatar da sake zaɓen ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2024, bayan da wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ce suka tarwatsa sake gudanar da zaben a wasu rumfunan zabe da dama a kananan hukumomin biyu.
A shekarar 2023 ce Kotun Daukaka kara ta soke zaben dan Majalisar Dokoki na Jam’iyyar APC mai wakiltar mazabar, Alhaji Garba Ya’u Gwarmai, biyo bayan kalubalantar nasarar da ya samu a shari’a da Alhaji Yusuf Ali Maigado na Jam’iyyar NNPP ya shigar.
Kotun ta bayar da umarnin a sake yin zabe cikin kwanaki 90.
Da yake tsokaci kan rashin wakilcin da mazabar ta daɗe ba ta da shi, masanin harkokin siyasa, Dokta Kabiru Sufi ya ɗora alhakin lamarin ga Hukumar Zabe ta kasa da kuma ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki daga mazabar, yana mai zargin su da gazawa wajen ganin an gudanar da zaben cikin lumana da kwanciyar hankali.
“Masu ruwa da tsaki a yankin suna da hujjar tambayar Hukumar Zabe ta kasa dalilin da ya sa ta gaza kammala aikin gudanar da zaben kamar yadda doka ta tanada,” in ji Dokta Sufi.
Wani mazaunin yankin Malam Muhammad Tsamiya ya koka da rashin samun wakilci, inda ya bukaci gwamnan jihar da ya tabbatar da cewa ba a yi watsi da mazabar ba, musamman ganin yadda take fama da rashin isassun kayayyakin more rayuwa.
“Kunci yanki ne mai nisa, inda hatta malaman da aka tura domin gudanar da aikin nan sun ki zuwa saboda ba mu da hanyoyi ga matsalar ruwan sha da dai sauran matsaloli.
“Don haka a siyasance, gwamna shi ne wakilinmu tun da jihar baki ɗaya mazabarsa ce,” inji shi.
Ya zuwa yanzu dai Hukumar Zabe INEC ba ta sanar da wata rana ba da za a sake gudanar da zaben ba.
Da wakilinmu ya tuntubi shugabar kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a ta Hukumar Zabe ta Kasa, Hajiya Safiya ta bayyana cewa, idan hukumar ta shirya lokacin gudanar da zaben, kwamishinan Hukumar Zabe ta kasa, Ambasada Abdu Zango zai kira taron masu ruwa da tsaki domin tattauna tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓen.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Zaɓe gudanar da zaben Hukumar Zabe ta
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato
Sojoji sun yi nasarar cafke wani mutum da ake zargi dan ta’adda ne tare da gano ma’adanar makamai a yayin wani samame da suka yi a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.
Binciken farko ya nuna cewa wanda aka kama ɗin yana da alaƙa da wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ke da alhakin kisan wani makiyayi da satar shanu 1,250 a ƙauyen Tomborong, Ƙaramar Hukumar Riyom, a ranar 27 ga watan nan na Mayu.
A safiyar ranar Juma’a, sojoji suka kama wanda ake zargin, bayan samun rahoto game da inda ake zargin ɗan bangar yake ɓoye a ƙauyen Hura.
Yayin wani bincike da aka yi a maboyar wanda ake zargin, jami’an tsaro sun gano bindigar AK-47 guda daya, tare da harsasai 26 na 5.56mm da kuɗi da wasu abubuwan da ake zargin asiri ne.
Wata majiyar soji ta bayyana cewa wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro kuma yana “bayar da haɗin kai ga masu bincike kan sunaye da wuraren da sauran mambobin ƙungiyar da ma’adanar makamansu suke.”
Sojoji sun tsananta ƙoƙarin gano tare da kama sauran membobin ƙungiyar da ake zargi da alhakin ayyukan laifuka a yankin.