Aminiya:
2025-07-26@04:08:43 GMT

Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba

Published: 16th, February 2025 GMT

Shekara guda bayan da Hukumar Zabe (INEC) ta dakatar da sake zaben mazabar Tsanyawa da Kunci a Majalisar Dokokin Jihar Kano, yankin ya ci gaba da zama babu zaɓaɓɓen wakili da yake wakiltar su a Majalisar Dokokin jihar.

Hukumar Zabe ta Ƙasa ta dakatar da sake zaɓen ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2024, bayan da wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ce suka tarwatsa sake gudanar da zaben a wasu rumfunan zabe da dama a kananan hukumomin biyu.

Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno

A shekarar 2023 ce Kotun Daukaka kara ta soke zaben dan Majalisar Dokoki na Jam’iyyar APC mai wakiltar mazabar, Alhaji Garba Ya’u Gwarmai, biyo bayan kalubalantar nasarar da ya samu a shari’a da Alhaji Yusuf Ali Maigado na Jam’iyyar NNPP ya shigar.

Kotun ta bayar da umarnin a sake yin zabe cikin kwanaki 90.

Da yake tsokaci kan rashin wakilcin da mazabar ta daɗe ba ta da shi, masanin harkokin siyasa, Dokta Kabiru Sufi ya ɗora alhakin lamarin ga Hukumar Zabe ta kasa da kuma ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki daga mazabar, yana mai zargin su da gazawa wajen ganin an gudanar da zaben cikin lumana da kwanciyar hankali.

“Masu ruwa da tsaki a yankin suna da hujjar tambayar Hukumar Zabe ta kasa dalilin da ya sa ta gaza kammala aikin gudanar da zaben kamar yadda doka ta tanada,” in ji Dokta Sufi.

Wani mazaunin yankin Malam Muhammad Tsamiya ya koka da rashin samun wakilci, inda ya bukaci gwamnan jihar da ya tabbatar da cewa ba a yi watsi da mazabar ba, musamman ganin yadda take fama da rashin isassun kayayyakin more rayuwa.

“Kunci yanki ne mai nisa, inda hatta malaman da aka tura domin gudanar da aikin nan sun ki zuwa saboda ba mu da hanyoyi ga matsalar ruwan sha da dai sauran matsaloli.

“Don haka a siyasance, gwamna shi ne wakilinmu tun da jihar baki ɗaya mazabarsa ce,” inji shi.

Ya zuwa yanzu dai Hukumar Zabe INEC ba ta sanar da wata rana ba da za a sake gudanar da zaben ba.

Da wakilinmu ya tuntubi shugabar kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a ta Hukumar Zabe ta Kasa, Hajiya Safiya ta bayyana cewa, idan hukumar ta shirya lokacin gudanar da zaben, kwamishinan Hukumar Zabe ta kasa, Ambasada Abdu Zango zai kira taron masu ruwa da tsaki domin tattauna tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓen.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Zaɓe gudanar da zaben Hukumar Zabe ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Human Right Watch” ta yi kira ga gwamnatin sojan jamhuriyar Nijar da ta saki tsohon shugaban kasar Muhamad Bazum, wanda ake tsare da shi tun lokacin juyin mulkin watan Yuli na 2023.

Kungiyar ta kuma ce, ci gaba da tsare Muhammad Bazum da ake yi ba tare da yi masa shari’a ba, ya sabawa doka da kuma take dokokin kasa da kasa na sharia.

 Bayan juyin mulkin na 2023, shugabannin soja sun yi alkawalin gabatar da Bazum a gaban kotu domin yi masa shari’a bisa zargin cin amanar aksa.

A 2024, kotun musamman da aka kafa ta cirewa tsohon shugaban kasar rigar kariya, da hakan ya zama tamkar share fage domin yi masa sharia,sai dai har yanzu hakna ba ta faru ba.

Lauyoyin da suke bai wa Bazzoum kariya sun nemi taimakon kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada MDD da kungiyar tattalin arziki ta yammacin Afirka ( ECOWAS).

Dukkanin kungiyoyin na kasa da kasa da kuma na yammacin Afirka sun sha yin kira da a saki Bazzum ba tare da wani sharadi ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • ‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8
  • An kama budurwa mai shekara 19 da ake zargi da kashe yara 2 a Bauchi
  • Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa