Matsin Rayuwa: Mafi Akasarin Gwamnoni Sun Koma A Abuja – Ƙungiyar Ƙwadago
Published: 15th, February 2025 GMT
Ya ce Jihar Kogi ce ta gudanar da taron domin tana da shugabannin kungiyar a matsayin gwamna da mataimakinsa, inda ya ce Gwamna Usman Ododo na daya daga cikin jami’ansa a Jihar Neja sannan kuma mataimakin jami’in kungiyar malamai ta Nijeriya (NUT).
Ya ce, “Don haka muna son mu yi wannan taron ne domin mu saurare ku don sanin abin da aka yi da abin da ba a yi yadda ya kamata ba, don haka mu dauka mu kai musu.
“A gare mu, kamar zuwan gida ne. Muna so mu zo mu yi hulda da su don gano ko suna yin abubuwan da muke sukar wasu.”
Kan haramta kungiyoyin kwadago a kwalejojin jihar da gwamnatin baya ta Yahaya Bello ta yi kuwa, shugaban NLC ya nuna damuwa da cewa gwamnati ba ta da ikon haramta kungiyoyin da suke karkashin jeri na musamman na majalisa.
কীওয়ার্ড: Kungiyar Kwadago Matsin Rayuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna
Fitacciyar mai girkin nan, Hilda Effiong Bassey, wadda aka fi sani da Hilda Baci, ta sake kafa tarihi a duniya ta hanyar girka tukunyar dafa-dukar shinkafa mafi girma bayan shafe awa takwas tana girkin.
Hakan dai na ƙunshe ne cikin wani saƙon taya murna da Kundin Bajinta na Guinness ya wallafa a shafukan sada zumunta.
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCOHilda Baci dai ta dafa shinkafa dafa-duka mafi yawa a tarihi tare da sauran kayan haɗi da sunadaran ɗanɗano wadda nauyinta ya kai kilo 8,780 a yankin Victoria Island da ke Legas.
A shekarar 2023 Hilda mai shekaru 28 ta shiga Kundin Bajinta na Guiness World Record bayan shafe awa 93 da mintuna 11 tana girke-girken abinci iri-iri.
A wannan karon, Hilda ta girka ƙananan buhuna 200 na shinkafa wanda nauyinsu ya kai kilo 4,000 da katan 500 na tumatir da kilo 600 na albasa da sauran kayan haɗi.
An gudanar da zaman girkin a fili a cikin birnin kasuwanci na Legas, lamarin da ya ja hankalin ɗaruruwan masu kallo.
Dafa-dukar shinkafa wadda a wasu harsunan ake kira Jollof rice abinci ne da ake sha’awa sosai a yankin Yammacin Afirka, inda ƙasashe kamar Nijeriya, Ghana, Senegal, Kamaru, da Gambiya ke da’awar cewa su ne ke da mafi ƙwarewa a wurin girka ta.
A shekarar 2023, Hukumar Ilimi, Kimiyya, da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO) ta amince da Senegal a matsayin wurin da wannan abinci na dafa-dukar shinkafa ta samo asali.