Leadership News Hausa:
2025-05-22@13:38:52 GMT

Nazari A Kan Noman Agwaluma

Published: 15th, February 2025 GMT

Nazari A Kan Noman Agwaluma

Har ila yau, nau’in Agwaluma na agbalumo ko kuma na Udara, na bukatar yi masa ban ruwa sosai, musamman don ya yi saurin nuna a cikin kasar noman da aka shuka shi.

Bugu da kari, idan manomi zai sayo Irin nomansa, ya tabbatar da ya sayo a gurin da aka fi sani, musamman don ya samu ingantacce kuma mai lafiya.

Ba  Ta Kariya Daga Kamuwa Da kwari Ko Sauran Cututtukan Da Ke Harbin Amfanin Gona:

Ana bukatar manomi ya tabbatar da yana ba ta kariya daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi mata illa bayan ana shuka ta, domin irin wadannan cututtukan ko kwarin na iya hana Irinta da aka shuka ruba a cikin kasar noman da aka shuka Irin.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Agwaluma Ke Kammala Girma?

Bayan an shuka Agwaluma, musamman Gona na fara fitar da ‘ya’yanta ne daga shekara biyar zuwa 10, inda kuma ake saran saiwar  jikinta, domin adana wa ta fi bukatar yanayin da ya kai ma’unin yanayi daga 60 zuwa 70.

Har ila yau, wasu sun yi hasashen cewa, ba za a iya yin noman Agwaluma a Nijeriya ba, amma maganar ba haka take ba; domin ana iya yin nomanta kuma ta yi kyau sosai har dimbin wacce za a yi hada-hadar kasuwancinta abin da kawai ake bukata shi ne, mayar da hankali kan shuka ta da aka yi da nuna kwarin gwiwa da kuma ba ta kulawar da ta dace.

Abubuwan Da Ya Kamata A Tanada Na Noman Agwaluma Don Samun Riba A Nijeriya

Samar Da Kyakkyawan Tsari:

Kafin ka fara yin nomanta, ka tabbatar ka tsara  yadda noman nata zai kasance, musamman domin kaucewa yin asara bayan ka  zuba jarinka a ciki.

Gyaran Gonar Shuka Ta:

Kafin ka shuka Irinta, ana bukatar ka tabbatar da kasar noman nata mai kyau ce.

Zabo Nau’in Da Ya Dace:

Na bukatar ka zabo daga cikin nau’ukanta biyu, wato na  Udara ko kuma na Agbalumo, inda ake iya gano su ta hanyar girmansu.

Amfanin na kai wa tsawon shekara takwas kafin ta kammala girma, inda kuma aka kara habaka nau’insa wanda zai iya girma bayan shekara uku.

Yadda Ake Girbe Agwaluma:

Akasari, ana  girbe ta ne a watan Disamba, sai dai a wannan lokaci, ba ta yin dadi sosai; saboda haka, ana so a bar ta a gonar da aka shuka ta har wani ruwan saman ya kara dukan ta kafin a girbe ta, inda ake  yi mata girbin bayan Ganyen ta ya rikide zuwa ruwan dorawa.

Tsara Dabarun Hada-Hadar Kasuwancinta:

Bayan an shuka ta ta girma, za a iya kai ta kasuwa don sayarwa, domin ana nuna ci gaba da batan ta a kasuwa ganin cewa, ana yawan yin amfani da ita. Haka kuma manomi, zai iya wallafa tallan ta a kafar yanar gizo, don masu bukata su gani su kuma saya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nazari

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakan da suka dace domin ganin cewa garin Marte bai koma hannun ’yan Boko Haram ba.

Zulum, ya kai ziyara garin Marte domin duba halin da ake ciki da kuma yadda za a tabbatar da zaman lafiya.

Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5

Kafin zuwansa, ’yan ta’adda sun sake karɓe iko da Marte bayan harin da suka kai a ranar Juma’a, inda mutane da dama suka tsere zuwa garin Dikwa.

Gwamnan, ya ce mutane kimanin 20,000 ne suka tsere daga Marte, wanda hakan ka iya kawo matsala musamman ga matasa da za su iya shiga cikin harkokin ta’addanci.

Ya ce: “Muna da alhakin kare Marte. Idan muka rasa wannan gari, za mu iya rasa sauran ƙananan hukumominmu.

“Don haka ina roƙon Gwamnatin Tarayya da sojojin Najeriya su haɗa hannu wajen kare wannan gari.”

Zulum, ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro domin kawo zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar Borno.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
  • Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila
  • Jirgin Karshe Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
  • Jagora: Jamhuriyar Musulunci Ba Ta Bukatar Izinin Wani Mahaluki Domin Tace Sanadarin Uranium
  • Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
  • NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • Iran Ta Ce Gabatar Da Bukatar Dakatar Da Tashe Makamashin Uranium Karshen Tattaunawar Da Amurka
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki