Shugaban Kasar Amurka Yace Kungiyar BRICS ta mutu
Published: 15th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana cewa kungiyar tattalin arziki ta BRICS ta mutu, saboda barazanar da yayi na karawa dukkan mambobin kungiyar kudin fito ko haraji na 100% na kayakin kasashensu dake shiga kasar Amurka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana cewa, maganar shugaban zai kara sabani a cikin kasashen kungiyar, ta BRICS wanda suke ganin Amurka ta mamaye al-amuran tattalin arziki a duniya.
An kafa kungiyar BRICS ne a shekara 2009 kuma kasashen da suka fara kafata sune, Brazil, Russia, India, da kuma China, amma daga baya kungiyar ta kara fadada, inda kasashen Afirka ta kudu, Iran, Habasha, da kuma Hadaddiyar daular Larabawa.
Bayan da kasar Rasha ta karbi shugabancin kungiyar na karba karba, tana son ta aiwatar da shirye-shirye har 250 don karfafa kungiyar.
Trump ya kara da cewa idan kasashen Brics suna son su yi wasa da dalar Amurka duk za’a bugesu da kudaden fito dara-bisa dari.
Yace idan yayi masu hada zasu dawo su roki Amurka ta daukewa masu, sun kashe kungiyar BRICS.
Masana sun bayyana cewa idan Brics ta ci gaba da wanzuwa zata zama barazana ga dalar Amurka a matsayin kudaden da ake ajiya da kuma musayar kudade da su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas aragchi da tokwransa na kasar Masar Badr Abdullati da kuma tokwaransu na kasar Omman Badr ben Hamad Al-Busaidi sun tattauna a tsakaninsu a birnin Oslo inda suka halattar taron tattaunawa ta 22th da ake gudanarwa a birnin na Oslo babban birnin kasar Norway.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa bangarorin biyu sun yi maganar rikice-rikicen da ke faruwa a yankin da kuma hanyar warwaresu.
Taron oslo na shekara shekara dai a wannan karon ya maida hankali ne kan abubuwan da suke faruwa a yankin Asiya da kuma hanyoyin da yakamata abi don rage halin da ake ciki a yankin. Musamman matsalar yaki da kima kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza da kuma yadda HKI ta sabawa dukkan dokokin kasa da kasa a yakin.
Jaridar The National ta kasar Amurka ta bada labarin cewa kasashen Iran da masar wadanda basa da dangantakar Diblomasiyya na kimani shekar 40 sun tattauna batun maida huldar jakadanci a tsakaninsu, inda daga cikin ministan harkokin wajen Masar ya bukaci a shafin hoton Khalid Islam buli wanda ya kashe tsohon shugabann kasar Masar a shekara 1980 wanda aka sanya a kan wani babban titi a birnin Tehran. Har yanzun dai ba’aji ta bakin gwamnatinn kasar Iran kan hakan ba.