Shugaban Kasar Amurka Yace Kungiyar BRICS ta mutu
Published: 15th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana cewa kungiyar tattalin arziki ta BRICS ta mutu, saboda barazanar da yayi na karawa dukkan mambobin kungiyar kudin fito ko haraji na 100% na kayakin kasashensu dake shiga kasar Amurka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana cewa, maganar shugaban zai kara sabani a cikin kasashen kungiyar, ta BRICS wanda suke ganin Amurka ta mamaye al-amuran tattalin arziki a duniya.
An kafa kungiyar BRICS ne a shekara 2009 kuma kasashen da suka fara kafata sune, Brazil, Russia, India, da kuma China, amma daga baya kungiyar ta kara fadada, inda kasashen Afirka ta kudu, Iran, Habasha, da kuma Hadaddiyar daular Larabawa.
Bayan da kasar Rasha ta karbi shugabancin kungiyar na karba karba, tana son ta aiwatar da shirye-shirye har 250 don karfafa kungiyar.
Trump ya kara da cewa idan kasashen Brics suna son su yi wasa da dalar Amurka duk za’a bugesu da kudaden fito dara-bisa dari.
Yace idan yayi masu hada zasu dawo su roki Amurka ta daukewa masu, sun kashe kungiyar BRICS.
Masana sun bayyana cewa idan Brics ta ci gaba da wanzuwa zata zama barazana ga dalar Amurka a matsayin kudaden da ake ajiya da kuma musayar kudade da su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
Ɗaya daga cikin jigo da suka kafa Jam’iyyar PDP, Farfesa Jerry Gana ya yi iƙirarin cewa tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi zai kayar da duk wani ɗan takara a jihohin Arewacin Najeriya idan ya tsaya takara a PDP.
Da yake bayabni a tashar talabijin ta Arise TV a ranar Laraba, Gana ya ce, “Ni mai nazari ne, kuma ina nazarin ra’ayoyi, a jihohin Arewa Peter Obi a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP zai doke duk wani ɗan takara, saboda mutanenmu suna da gaskiya.”
Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar KwastamPeter Obi ya fice daga Jam’iyyar PDP a watan Mayun 2022 inda ya jagoranci Jam’iyyar LP a zaɓen 2023.
Da yake waiwayen tushen PDP, jigon na PDP ya tunatar da ’yan Najeriya irin ƙarfin da jam’iyyar ke da shi da kuma rawar da take takawa wajen maido da mulkin dimokraɗiyya.
Ya ce, “Dole ne in shaida cewa mutane da yawa sun manta cewa an kafa Jam’iyyar PDP ne a matsayin ƙungiya mai zaman kanta, a shekarar 1998 aka kafa mu, sannan muka shiga zaɓe a 1999, muna cikin kowace rumfar zaɓe, domin mu ne muka ci zaɓen farko.
“Mutane da yawa sun manta cewa PDP ce ta lashe mafi yawan ƙananan hukumomi, lokacin da aka zo batun zaɓen shugaban ƙasa, mun ci zaɓen shugaban ƙasa, mun ci na majalisar dattawa, muka ci majalisar tarayya, mu ne ke riƙe da madafun iko, shi ya sa muka yi matuƙar farin ciki da cewa mun maido da dimokuraɗiyya a Najeriya, muka sake kafa mulkin farar hula.
“Saboda shekaru da dama ana mulkin soja, amma mun samu nasarar kawo ƙarshen hakan ta hanyar dimokuraɗiyya, don haka PDP ta kasance jam’iyyar talakawa ce, shi ya sa idan muka ce mulki ga jama’a, muna nufin hakan ne saboda abin ya kasance, kuma ya kasance haka.”