Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta
Published: 12th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya miƙa wa sabon Shehun Bama, Dakta Umar Kyari Umar El-Kanemi sandar sarauta, a wani biki da aka gudanar a filin wasa na garin Bama.
A yayin bikin, Gwamna Zulum ya yi alƙawarin kammala titin Maiduguri zuwa Banki domin bunƙasa harkokin kasuwanci tsakanin Najeriya, Kamaru da Chadi.
Haka kuma, ya ce gwamnatinsa za ta tabbatar da kammala Jami’ar Aikin Gona ta Tarayya da ke Bama da kuma dawo da wutar lantarki a yankin.
Zulum, ya ƙara da cewa za a ci gaba da tallafa wa masarautar da gyara gine-ginen da Boko Haram suka lalata.
Hakazalika, ya ce gwamnatinsa za ta taimaka wajen dawo da ’yan gudun hijira zuwa gidajensu.
A nasa jawabin, sabon Shehun Bama, Umar Kyari Umar El-Kanemi, ya gode wa gwamna Zulum bisa wannan matsayi da ya gaji daga mahaifinsa, Alhaji Ibrahim Umar Ibn Umar El-Kanemi, wanda ya shafe kusan shekaru 30 yana mulkin masarautar Bama.
An yi hawan dawaki, raye-rayen gargajiya, wake-wake da harbe-harben bindiga.
Manyan baƙi da suka halarta sun haɗa da Mataimakan Gwamnonin Borno da Yobe, Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, da sauran sarakuna da manyan jami’an gwamnati.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sabon Sarki Sandar Sarauta
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp