Aminiya:
2025-09-17@23:28:00 GMT

Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Published: 12th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya miƙa wa sabon Shehun Bama, Dakta Umar Kyari Umar El-Kanemi sandar sarauta, a wani biki da aka gudanar a filin wasa na garin Bama.

A yayin bikin, Gwamna Zulum ya yi alƙawarin kammala titin Maiduguri zuwa Banki domin bunƙasa harkokin kasuwanci tsakanin Najeriya, Kamaru da Chadi.

Dokokin gyaran haraji sun tsallake karatu na biyu a majalisa An yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga a Kaduna

Haka kuma, ya ce gwamnatinsa za ta tabbatar da kammala Jami’ar Aikin Gona ta Tarayya da ke Bama da kuma dawo da wutar lantarki a yankin.

Zulum, ya ƙara da cewa za a ci gaba da tallafa wa masarautar da gyara gine-ginen da Boko Haram suka lalata.

Hakazalika, ya ce gwamnatinsa za ta taimaka wajen dawo da ’yan gudun hijira zuwa gidajensu.

A nasa jawabin, sabon Shehun Bama, Umar Kyari Umar El-Kanemi, ya gode wa gwamna Zulum bisa wannan matsayi da ya gaji daga mahaifinsa, Alhaji Ibrahim Umar Ibn Umar El-Kanemi, wanda ya shafe kusan shekaru 30 yana mulkin masarautar Bama.

An yi hawan dawaki, raye-rayen gargajiya, wake-wake da harbe-harben bindiga.

Manyan baƙi da suka halarta sun haɗa da Mataimakan Gwamnonin Borno da Yobe, Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, da sauran sarakuna da manyan jami’an gwamnati.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sabon Sarki Sandar Sarauta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

 

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara