Zanga-zanga ta ɓarke kan hare-haren ’yan bindiga a Kaduna
Published: 12th, February 2025 GMT
Mazauna Ungwan Ate da ke Ƙaramar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna, sun fito kan tituna domin yin zanga-zanga kan yawaitar hare-haren ’yan bindiga da satar jama’a da suka addabi yankinsu.
Masu zanga-zangar sun toshe hanyar Ungwan Ate zuwa Ungwan Mission da ke kan babbar hanyar Kaduna zuwa Kachia.
Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – MatashiSun kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don kare rayukansu da dukiyoyinsu.
Wani daga cikin masu zanga-zangar da ya zanta da Aminiya, ya ce ’yan bindiga sun shiga Ungwan Ate a daren ranar Talata, inda suka shafe sama da sa’o’i biyu suna cin karensu ba babbaka, tare da sace mutum ɗaya daga ƙauyen.
“Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.
“’Yan bindiga suna yawan kawo mana hari a duk lokacin da suka ga dama. Gwamnati da hukumomin tsaro su gaggauta ɗaukar mataki kafin mu ƙare,” in ji shi.
Wani mazaunin yankin ya ce matsalar tsaro a Kachia ta kai ga mutane ba sa iya zuwa gonakinsu ko barci cikin kwanciyar hankali.
“Gwamnati ta ce ta yi sulhu da ‘yan bindiga, amma kullum ana kashe mu a Kachia.
“Mutane da dama na cikin daji suna shan wahala kan laifukan da ba su san komai a kansu ba,” in ji shi cikin fushi.
Masu zanga-zangar sun ce ’yan bindiga sun mayar da yankin filin daga, lamarin da ya sa suka tsinci kansu cikin tsananin fargaba da damuwa.
“Ba ma iya zuwa gona, alhali yawancinmu da noma muka dogara,” in ji wani daga cikin masu zanga-zangar.
“Ba ma iya yin barci cikin kwanciyar hankali. Ana so a ƙarar da mu ne?”
Zanga-zangar ta biyo bayan hare-hare da yawaitar sace-sacen mutane a Ƙaramar Hukumar Kachia.
Ƙauyuka irin su Gadanji, Ungwan Wage, Ungwan Alhaji, Agunu Dutse, Maro da Ungwan Dauje na fama da hare-haren ’yan bindiga ba dare ba rana.
Mazauna yankin sun ce duk da kiraye-kirayen da suke yi ga mahukunta, babu wani matakin tsaro da aka ɗauka domin kare su daga hare-haren.
A halin da ake ciki, mazauna yankin na ci gaba da roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su kawo musu ɗauki domin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai amsa kiran waya ba.
Ga hotunan yadda zanga-zangar ta gudana:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare Tsaro zanga zangar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
Ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta sanar da cewa daga lokacin da aka tsayar da wuta zuwa yanzu adadin Falasdinawan da HKI ta kashe sun kai 200, yayin da wasu kusan 600 sun jikkata.
Sanarwar ta ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta kuma ci gaba da cewa; A cikin sa’o’i 48 da su ka gabata,an sami shahidai 22, biyar daga cikinsu basu dade da yin shahada ba, sai kuma 17 da aka tono su daga karkashin baraguzai. Haka nan kuma na kai wasu 9 zuwa asibitocin da suke a yankin.
Wani sashe na sanarwar ma’aikatar kiwon lafiyar ta Gaza ya ce, har yanzu da akwai shahdai masu yawa da suke a karkashin baraguzai, wasu kuma a kan hanyoyi, saboda rashin kayan aiki da kungiyoyin agaji za su yi amfani da su.
Tun daga ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu, adadin shahidai ya kai 68,858, sai kuma wani adadin da ya kai 170,664 da su ka jikkata.
Amma daga tsayar da wuta a ranar 11 ga watan Oktoba zuwa yanzu, an sami shahidai da sun kai 226, sai kuma wasu 594 da su ka jikkata. Haka nan kuma an iya tsamo gawawwakin shahidai daga cikin baraguzai har su 499.
Haka nan kuma ma’aikatar kiwon lafiyar tra sanar da karbar gawawwaki 30 da HKI ta mika wa bangaren Falasdinawa ta hannun hukumar agaji ta “Red-Corss.
Tun bayan tsagaita wutar yaki, har ya zuwa yanzu dai HKI tana ci gaba da kai hare-hare a sassa daban-daban na Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci