Aminiya:
2025-09-18@08:25:39 GMT

Zanga-zanga ta ɓarke kan hare-haren ’yan bindiga a Kaduna

Published: 12th, February 2025 GMT

Mazauna Ungwan Ate da ke Ƙaramar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna, sun fito kan tituna domin yin zanga-zanga kan yawaitar hare-haren ’yan bindiga da satar jama’a da suka addabi yankinsu.

Masu zanga-zangar sun toshe hanyar Ungwan Ate zuwa Ungwan Mission da ke kan babbar hanyar Kaduna zuwa Kachia.

Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – Matashi

Sun kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don kare rayukansu da dukiyoyinsu.

Wani daga cikin masu zanga-zangar da ya zanta da Aminiya, ya ce ’yan bindiga sun shiga Ungwan Ate a daren ranar Talata, inda suka shafe sama da sa’o’i biyu suna cin karensu ba babbaka, tare da sace mutum ɗaya daga ƙauyen.

“Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.

“’Yan bindiga suna yawan kawo mana hari a duk lokacin da suka ga dama. Gwamnati da hukumomin tsaro su gaggauta ɗaukar mataki kafin mu ƙare,” in ji shi.

Wani mazaunin yankin ya ce matsalar tsaro a Kachia ta kai ga mutane ba sa iya zuwa gonakinsu ko barci cikin kwanciyar hankali.

“Gwamnati ta ce ta yi sulhu da ‘yan bindiga, amma kullum ana kashe mu a Kachia.

“Mutane da dama na cikin daji suna shan wahala kan laifukan da ba su san komai a kansu ba,” in ji shi cikin fushi.

Masu zanga-zangar sun ce ’yan bindiga sun mayar da yankin filin daga, lamarin da ya sa suka tsinci kansu cikin tsananin fargaba da damuwa.

“Ba ma iya zuwa gona, alhali yawancinmu da noma muka dogara,” in ji wani daga cikin masu zanga-zangar.

“Ba ma iya yin barci cikin kwanciyar hankali. Ana so a ƙarar da mu ne?”

Zanga-zangar ta biyo bayan hare-hare da yawaitar sace-sacen mutane a Ƙaramar Hukumar Kachia.

Ƙauyuka irin su Gadanji, Ungwan Wage, Ungwan Alhaji, Agunu Dutse, Maro da Ungwan Dauje na fama da hare-haren ’yan bindiga ba dare ba rana.

Mazauna yankin sun ce duk da kiraye-kirayen da suke yi ga mahukunta, babu wani matakin tsaro da aka ɗauka domin kare su daga hare-haren.

A halin da ake ciki, mazauna yankin na ci gaba da roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su kawo musu ɗauki domin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai amsa kiran waya ba.

Ga hotunan yadda zanga-zangar ta gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare Tsaro zanga zangar yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro

 Babban sakataren majalisar koli ta tsaron jamhuriyar musulunci ta Iran Dr. Ali Larijani ya bayyana cewa; Za a bunkasa aiki tare a tsakanin Iran da Saudiyya a fagagen tattalin arziki da kuma tsaro.

Dr. Larijani ya bayyana hakan ne jim kadan bayan fitowar daga ganawar da ya yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mu8hammad Bin Salman.

Bugu da kari Dr. Ali Larijani ya ce a yayin ganawarwa da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman, sun tattauna hanyoyin bunkasa alakar kasashensu ta fuskoki mabanbanta, da kara girman wannan alakar ta fuskar tattalin arzki da tsaro fiye da yadda take a yanzu.”

Haka nan kuma ya ce, za a yi aiki domin kawar da dukkanin abubuwan da suke kawo cikas a kan hanyar bunkasa wannan alakokin.

Dr. Ali Larijani ya kuma ce,an yi shawara akan yadda kasashen yankin za su bunkasa alakarsu ta tsaro domin ganin an tabbatar da zaman lafiya.

Da aka tambaye shi akan ko an sami sauyi akan mahangar kasashen Larabawa bayan harin da HKI ta kai wa Qatar, Dr.Ali Larijani ya ce; Tabbas da akwai sauyi a cikin yadda kasashen larabawa suke Kallon abubuwan da suke faruwa, domin suna ganin cewa kasantuwar HKI a cikin wannan yankin yana hana zaman  lafiya.

Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya ziyarci Saudiyya inda ya gana da ministan tsaronta da kuma Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza September 17, 2025 Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi