Aminiya:
2025-05-01@04:47:31 GMT

Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga

Published: 10th, February 2025 GMT

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya bayyana cewa sharaɗinsa na sulhu da ’yan bindiga shi ne kawai su daina kashe-kashe su zubar da makamai sannan su miƙa wuya.

A baya dai Gwamna Dare ya sha nanata cewa ba zai yi sulhu da ’yan fashin daji ba.

Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri

Ko a watan Yulin 2024, sai da wani mai magana da yawunsa, Alhaji Faruk Ahmad, ya bayyana cewa babu wani matsin lamba da zai sa gwamnatinsu ta yi sulhu da ’yan ta’addan.

Ya kuma jaddada cewa mataki ɗaya da gwamnatin ta ɗauka wanda kuma yana haifar da ɗa mai ido shi ne yaƙar ’yan bindigar amma babu batun sulhu.

Sai dai a hirarsa da BBC, Gwamnan ya bayyana cewa ba wai ba za a iya yin sulhu da ’yan bindigar ba ne, “amma ko da za ka yi sulhu ka yi shi a kan gaskiya, ai.

“Akwai da yawa waɗanda aka cutar da su, wasu an kashe iyayensu wasu matansu, saboda haka sai a duba me za a yi masu saboda sun rasa dukiyarsu, bawai kullum a riƙa fitfita ƴanbindiga ba,” in ji Dauda.

Ya ƙara da cewa sai ’yan bindigar sun daina kashe mutane kuma sun ajiye makamansu sannan za a iya yin sulhu da su.

Gwamna Dauda ya bayyana cewa suna samun nasara a yaƙin da suke da ƴanbindiga, “An kashe ’yan ta’adda fiye da 50 a ranar Juma’a a garin Tingar Fulani, wajen Zurmi da Shinkafi.

“Akwai manya-manyan kachalloli da yanzu haka sun tafi lahira, waɗanda suke tare da Bello Turji, akwai Sani Mainasara da Sani Black da Kachallah Auta, Audu Gajere da Kabiru Jangero, Dangajere da makamantansu, duk an hallaka su,” a cewar Dauda Lawal.

Gwamnan ya ce wannan nasara da ake samu za a ci gaba da samunta “har sai na kai ƙarshen lamarin. Ko dai su ajiye makamansu ko kuma mu ba za mu bar su ba.”

Matsin lamba ya sa ’yan bindiga neman sulhu — Makama

Fitaccen mai sharhi kuma masani akan sha’anin tsaro Zagazola Makama ya bayyana cewa matsin lamba da sojoji ke yi wa ’yan bindiga ya sa suke neman sulhu.

Zagazola ya bayyana haka a shafinsa yayin da yake sharhi akan wani faifan bidiyo da yake yawo, inda aka ji Bello Turji da wani shahararren malami a Zamfara, suna tattaunawa akan yadda ɗan bindigar zai ajiye makamai.

A baya-bayan nan, manyan ’yan bindiga da dama sun bayyana aniyarsu ta ajiye makamai sun rungumi zaman lafiya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Dauda Lawal Dare Jihar Zamfara ya bayyana cewa yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Mista Mark Joseph Carney murna bisa zaɓensa a matsayin Firaiminista na 24 na ƙasar Kanada, bayan nasarar jam’iyyar Liberal a zaɓen majalisar dokokin da aka kammala kwanan nan.

 

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana zaman Carney a wannan matsayi a matsayin wani muhimmin ci gaba, musamman a wannan lokaci da Kanada ke bukatar gogaggen shugaba domin fuskantar ƙalubale da dama.

 

Carney, wanda fitaccen masani ne a fannin tattalin arziki, ya taba rike mukamin Gwamnan Babban Bankin Kanada daga shekarar 2008 zuwa 2013, sannan ya ci gaba da zama Gwamnan Babban Bankin Ingila daga 2013 zuwa 2020.

 

Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa ƙwarewar sabon shugaban Kanada a fannin kuɗi da shugabanci za ta taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar ƙasar. Haka kuma, ya sake jaddada kudirin Najeriya na ƙarfafa dangantakar diflomasiyya da Kanada, musamman a fannonin ilimi, sauyin yanayi da hijira.

 

Shugaban Najeriya ya ƙara da cewa yana fatan kafa kyakkyawan hadin gwiwa da gwamnatin Carney, yayin da ya nuna godiyarsa ga kyakkyawar alakar da aka kula a tsakaninsu  a zamanin tsohon Firayim Minista, Justin Trudeau.

 

Bello Wakili

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara