’Yan daba sun ƙona gine-ginen makaranta a Binuwai
Published: 10th, February 2025 GMT
Wasu ’yan daba sun gine-ginen makaranta a yankin Okpoga da ke Karamar Hukumar Okpogwu da ke Jihar.
Ɓata-garin sun ƙona gine-ginen ne a Makarantar Sakandaren Central UBE da ke Ogwu-Okpoga da kuma Makarantar Ƙaramar Sakandare s ake Obossa.
Wani shaida ya bayyana wa wakilinmu cewa a makon da ya gabata ne ’yan daban suka yi wannan aika-aika.
Kokarinmu ma ji daga kakakin ’yan sanda ta Jihar Binuwai, Catherine Aneneh, bai yi nasara ba, saboda mun kira ta a waya ba ta shiga ba.
’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya?Amma a ƙarshen mako ɗan Majalisar Dattawa mai wakiltar Binuwai ta Kudu kuma Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dattawa, Sanata Abba Moroh, ya ziyarci makarantun da abun ya shafa a ƙarshen mako.
Abba Moroh ya yi tir da lamarin tare da mamakin dalilin ƙona cibiyoyin ilimi da ake rainon manyan gobe.
Daga nan sai ya yi alƙawarin sake gina ajujuwan yana mai kira ga al’ummar yankin da su tashi domin kare ababen more rayuwar da aka samar musu.
Dan majalisar ya kuma ziyarci babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Yankin Okpoga, inda ya jinjiya musu bisa ƙoƙarinsu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Sai dai ya koka bisa mummunan halin da ofishin yake ciki, sannan ya yi alƙawarin yi masa kwaskwarima.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ɗaukar matakai masu tsauri kan duk wanda aka samu da hannu a harkar fasa bututun mai da satar ɗanyen mai a yankin Niger Delta. Daraktan Tsaron Makamashi a Ofishin Mai baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (ONSA), Hon. Ojukaye Flag-Amachree, ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da kamfanin Pipeline Infrastructure Nigeria Limited (PINL) ya shirya a birnin Fatakwal.
A cewarsa, tuni sama da mutum 100 da ake zargi da hannu a wannan haramtacciyar harka an gurfanar da su a gaban kotu. Ya ce duk wanda aka kama, komai muƙaminsa, za a hukunta shi bisa doka. Ya kuma roki shugabannin al’umma da su ja kunnen matasa da yara kada su shiga lalata bututun mai.
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A JigawaYa ce: “Muna roƙonku da ku yi magana da ‘yan uwanmu. Muna sanin mutanen da ke wannan harka, ku shawarce su su daina. Yanzu abubuwa ba kamar da ba ne. Fiye da mutum 100 tuni an hukunta su. Ko kai Soja ne, ko Janar ne, muddin aka same ka da laifi, za ka fuskanci hukunci.”
A nasa ɓangaren, Jami’in hulɗa da jama’a na PINL, Tarilah Alamieseigha, ya bayyana cewa kamfanin ya amince da bayar da tallafin karatu har guda 646 da wasu ƙarin shirye-shirye ga al’ummomi 215 da ke kusa da bututun Trans Niger Pipeline (TNP). Ya yaba da haɗin kan da ke tsakanin kamfanin da al’ummomi, wanda ya taimaka wajen bunƙasa samar da mai a ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp