Pezeshkian : Iran Za Ta Dakile Duk Wasu Makirce-makircen Makiya
Published: 10th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi kokarin dakile duk wani makirce-makircen da makiya ke kitsawa.
Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a shekara ta 1979 a birnin Tehran yau Litinin.
Shugaba Pezeshkian Ya soki ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan na cewa yana son tattaunawa da Iran yayin da a lokaci guda ya ba da umarnin kakaba wa Iran takunkumi kan man da take fitarwa zuwa sifiri.”
Trump ya yi ikirarin cewa Iran na kawo cikas ga tsaron yankin amma “Isra’ila ce, tare da goyon bayan Amurka, tushen duk wani rashin tsaro a yankin da jefa kisan kiyashi a Gaza, hare-hare a kasashen Lebanon, Siriya, Iran da kuma duk inda ta ga dama.”
Pezeshkian ya yi gargadin cewa makiya suna neman haifar da fitina a cikin Iran, Sai dai kuma ba su san cewa a karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei da kuma irin sadaukarwar da al’ummar Iran suke yi, za’a kawo karshen duk wannan mafarki.
Shugaban na Iran ya kara da cewa, Iran ba ta taba neman kaddamar da yaki kan wata kasa ba, kuma ba za ta taba mika wuya ga makiya ba.
Iran ba za ta taba barin makiya su aiwatar da munanan manufofinsu ba, in ji shugaba Pezeshkian.
Ya nanata kudurin Iran na samun zaman lafiya tare da makwabtanta bisa ‘yan uwantaka da mutunta juna, game da batun Gaza kuma, muna kare wadanda ake zalunta ne inji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.
Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.
Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.
A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.
“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.
Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.
Tinubu ya kuma yaba wa masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.
Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.
Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.
Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.
Daga Bello Wakili