Wakilin Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci A Iraki Ya Ya Jaddada Rawar Juyin Juya Halin Musulunci
Published: 9th, February 2025 GMT
Wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya ce: Juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon samfuri na hadin kan al’umma
Ayatullah Mojtaba Hosseini, wakilin Jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki ya bayyana muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma nauyin da ya rataya a wuyan musulmi na daidaiku da na al’umma dangane da manufofin juyin juya halin Musulunci, yana mai cewa: juyin juya halin Musulunci ya gabatar da wani sabon salo na hadin kan al’ummar musulmi.
A jawabin da ya gabatar na zagayowar samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran da aka gudanar a tsohon gidan da Imam Khumaini (r.a) da ya zaune a birnin Najaf, Ayatullah Husaini ya jaddada muhimmancin hadin kan al’ummar musulmi da kuma irin nauyin da ke wuyan musulmi na daidaiku da na zamantakewa da suka dace da manufofin juyin juya halin Musulunci.
Har ila yau Ayatullah Mojtaba Hosseini ya tabo batun juyin juya halin Musulunci a Iran yana mai bayyana hakan a matsayin wata mu’ujiza ta Ubangiji, sannan ya kara da cewa: Batun juyin juya halin Musulunci yana nan a kan tafarkinsa kuma Allah ya nufa ya zama wani gagarumin yunkuri na jama’a wanda ya iya haifar da gagarumin sauyi a Iran da kuma duniyar musulmi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: juyin juya halin Musulunci a
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya zargi Isra’ila da yin zagon kasa ga diflomasiyya ta hanyar tsallaka jajayen layukan kasar Iran, da kuma ta’azzara rikici da kasashen yammacin duniya, yana mai bayyana cewa, ba za a iya yin shawarwari a halin da ake ciki ba.
Sanarwar dai na nuni da koma baya sosai a yunkurin diflomasiyya na Iran da kasashen Yamma, musamman yadda tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara bayan matakin sojin Isra’ila.
Matakin na Isra’ila da hadin kai tare da Amurka na a matsayin kokari na kawar da duk wata dama ta cimma sakamakon shawarwari.
“Ba za a iya shawarwarin ba yayin da a lokaci guda ake barin gwamnatin kisan kare dangi ta kai hari kan Iran.”
“Ba Isra’ila za ta aikata irin wadannan laifuka ba tare da amincewar Amurka ba.”
Iran dai na kallon hare-haren da Isra’ila ta kai a baya-bayan nan a matsayin wani hari kai tsaye ga ‘yan kasarta.